• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno

by Muhammad and Leadership Hausa
10 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2024: Fasto Umo Bassey Eno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fasto Umo Bassey Eno ya samu lambar yabo ta Gwarzon Gwamnan Shekara ta 2024 ta Jaridar Leadership, saboda jagorancinsa na hangen nesa da kuma saurin aiwatar da tsare-tsaren Noma da Ci gaban Karkara da samar da Ababen More Rayuwa, Tsaro da Ƙarfafa Wa Jama’ar jiharsa (ARISE Agenda).

Wannan Shiri (ARISE Agenda) ya shafi ɓangarori masu muhimmanci kamar lafiya da ilimiilimi da tattalin arziƙi da samar da ayyukan yi da sauransu, wanda ya hakan ya yi tasiri a Jihar Akwa Ibom cikin watanni 15 kacal na mulkinsa. Ta hanyar ayyana muradunsa a fili da cimma nasarori masu gamsarwa, Fasto Eno, ya tabbatar da cancantarsa na samu wannan babbar lambar yabo.

  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Umo Eno shi ne gwamnan farar hula na huɗu a tarihin Jihar Akwa Ibom mai shekaru 37 tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a shekarar 1999. Fasto ne a Cocin All Nations Ministry International Church, bayyanarsa a matsayin gwamna abin mamaki ne, wanda ya sa ake masa laƙani da “Golden Boy” saboda kyawun fuskarsa da kuma tafiyar siyasarsa mai cike da al’ajabi. An gano bajintarsa a siyasance ta hannun, tsohon Gwamna Udom Emmanuel, wanda Eno ya fara siyasarsa ta hanyar zama Kwamishinan filaye a jihar.

A lokacin da tsohon Gwamna Udom Emmanuel ya kusa barin mulki, ba tare da ɓata lokaci ba ya zaɓi Eno a matsayin wanda zai gaje shi duk da yawan masu neman wannan matsayi. Wannan sanarwa ta girgiza mutane da dama da suke tsammanin zaɓar wanda ya yi fice a siyasar jihar. Duk da haka, Eno ya samu karɓuwa sosai, ba kawai daga Kiristoci da abokan tsohon gwamnan ba, har ma daga jama’ar Akwa Ibom da yawansu ya kai miliyan 7.2. Duk da cewa akwai shakku a zukatan wasu saboda rashin daɗewarsa a harkar siyasa, amma ya kawar da wannan shakkun ta hanyar juriya da jagorancinsa.

Ko da yake ya fuskanci zarge-zarge a siyasa, ciki har da kiransa da “wanda bai da ilimi,” Eno ya fuskanci kalubalen, ta hanyar jajircewa da ƙwarewa a matsayinsa na shugaba. Tafiyarsa a harkar siyasa, wanda ba kasafai aka san shi da ita ba, ta zama misalin yadda mutum zai iya nasara duk da ƙalubalen da zai fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

A ranar 29 ga watan Mayu, 2023, lokacin rantsar da shi, Eno ya bayar da labarin rayuwarsa mai ban sha’awa, inda ya ruwaito yadda ya tashi cikin ƙunci a matsayin ɗan wani ɗan sanda da kuma mahaifiya mai ƙoƙarin kula da iyalanta bayan mutuwar mahaifinsa. Ya tashi a barikin ‘yansanda, ya yi karatu da sayar da lemo a Filin Jirgin Sama na Legas domin tallafa wa mahaifiyarsa da ‘yan uwansa. Ya ruwaito cewar, “Da wani ya faɗa min zan zama gwamna, da na ce masa ya je asibiti domin tabbas yana fama da ciwon maleriya mai tsanani ko kuma ya ruɗe.” Yau, mutumin da ya tashi a wannan yanayi ya zama gwamnan Jihar Akwa Ibom a zahiri.”

Mulkin Eno ya tabbatar da alƙawarin jagoransa, Udom Emmanuel, wanda ya ce, “Mutumin da zai zo bayana zai yi abubuwa masu tasiri sama da waɗanda na yi.” Ta hanyar tsarin ARISE Agenda, Gwamna Eno ya mayar da hankali kan samar da abinci da samar da ayyukan yi da kuma samar da tsaro mai inganci, wanda ya mayar da Akwa Ibom wata mafaka ga masu yawon buɗe ido da masu zuba jari da kuma baƙi.

Wannan ci gaba ya bunƙasa samun kuɗaɗen shiga na jihar, wanda ya ƙara mata matsayi a matsayin babbar jiha mai arziƙi a yankin Neja Delta.

Nasarar da Gwamna Eno ya samu ta ja hankalin mutane da dama, har ma a matakin ƙasa. Duk da cewa Akwa Ibom tana ƙarƙashin mulkin jam’iyyar adawa, ya samu haɗin kai daga manyan mutane irin su Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio. Jagorancinsa ya kawo ƙarshen rigingimun siyasa da suka daɗe suna hana Jihar Akwa Ibom samun ayyukan gwamnatin tarayya da wasu tallafi, inda ya kawo wani sabon salo na haɗin kai da ci gaba a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiUmo Bassey Eno
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Next Post

Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu’amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

Related

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

8 minutes ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

2 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

4 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

5 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

9 hours ago
Next Post
Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu’amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

Gwarzon Shekara Wajen Sauƙaƙa Mu'amalar Kuɗaɗe A 2024: OPay

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.