• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
China

Kasar China ta kasance ta gaba gaba a fannin noman tumatir a duniya. Musamman a jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar, an fi noman tumatir sabo da jihar tana da wani irin yanayi wanda tumatir yake bukata. Sama da kashi 30% na yawan tumarin da ake samarwa a kasuwar duniya yana fitowa ne daga China. Harkar noman tumatir yana habaka cikin sauri, musamman idan aka yi la’akari da yadda nau’in tumatirin China ya fi na sauran kasashe inganci. Sabo da kyawo da inganci da kuma rahusa ya sanya tumatirin kasar China ya samu karbuwa a yawancin gidajen abinci na kasashen yammacin duniya.  

Sakamakon rikice-rikice da wasu yankuna na duniya suka samu kansu a ciki ya sanya farashin amfanin gona ya yi matukar hauhawa a kasuwannin duniya, ciki kuwa har da tumatir. To amma duk da hauhawar farashin, ana samun tumatirin kasar China cikin sauki da rahusa, abin da ya sanya ya kara samun karbuwa a kasuwar duniya.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bikin Kaddamar Da Aikin Layin Dogo Na Sin- Kyrgyzstan-Uzbekistan
  • Ma’aikatar Kananan Hukumomi A Zamfara Ta Gabatar Da Bitar Kasafin Kudin Kananan Hukumomi 

Wannan lamari na karbuwar da tumatirin China ya samu a duniya ya tsonewa Amerika da kasashen yammaci ido, har ta kai ga suna kulla makirci da yada karerayi game da tumatirin na kasar China, inda suke cewa wai China na amfani da tsarin tursasawa da bautarwa a gonakin tumatir dake jihar Xinjiang. Wasu kafafen yada labaru na yammcin duniya, wadanda su ne karnukan farautar Turai da Amerika suna yayata cewa wai ana tursasawa musulmi ’yan kabilar Uygur suna aikin bauta a gonakin tumatir na lardin Xinjiang.

Irin wadannan karerayi da kafafen yada labarun na Turai ke yadawa, ko kadan babu kamshin gaskiya a cikinsu, illa iyaka hassada ce kawai da ganin kyashi bisa ga yadda kasar ta China take samun ci gaba a fasahar noma.

A bayyane take cewa irin ci gaba da China ta samu a fannin fasahar noma, ba ta bukatar yin amfani da mutane a matsayin leburori, ballantama a ce ta tursasa masu yin aikin karfi a gonakin tumatir. Domin kuwa tun daga matakin dashe har zuwa matakin girbi, na’ura ce ke yin komai. Aikin da leburori 150 za su yi a cikin yini daya, na’ura guda za ta yi shi a cikin yini daya.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Akwai wasu ‘yan tsirarrun mutane da irin wadannan kafafen yada labaru na yammaci suke ba su kudi domin su yi ikirarin cewa su al’ummar Xinjiang ne, a yi hira da su, inda za su rinka yin ikirarin cewa mahukunta a China suna tilasta masu aikin bauta a gonakin tumatir a jihar Xinjiang, alhali kuwa irin wadannan mutane ko hanyar Xinjiang ba su sani ba.

Kafafen yada labarun na yammaci wadanda ke babatu kare hakkin dan Adam, sun kasance masu kara jefa mutane cikin rashin aikin yi da talauci. Babu irin kokarin da irin wadannan kafafen yada labaru na kasashen yammaci ba su yi ba na yin batanci ga kasar China, amma duk a banza. Misali, akwai wata kafar yada labaru ta yammaci da ta kirkiro wani shiri na musamman kan bin diddigin inda ake sayar da tumatirin da ake nomawa a jihar Xinjiang. Sun bi masana’antun sarrafa tumatirin gwangwani, kamar Petti da Derica, suna daukar samafari domin yin gwaji ko akwai nau’in tumatirin da ake nomawa a jihar Xinjiang, amma sakamakon duk gwaje-gwajen nasu bai zo daidai da hakikanin gaskiyar abin da suke zargi ba.

Sabo da haka, batun bautar da leburori, ko kuma tilasta masu yin aikin karfi a gonakin tumatir a jihar Xinjiang magana ce wadda hankali ba zai dauka ba, musamman idan aka yi la’akari da dokokin da ke kare hakkin leburori wadanda China ke bi sau da kafa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Next Post
Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

Hukumar KNARDA Ta Horar Da Manoman Wake Tare Da Ba Su Kayan Aiki A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
China

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.