• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jigon APC Ya Fara Yunkurin Sulhunta Kwankwaso, Ganduje Da Shekarau

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jigon APC Ya Fara Yunkurin Sulhunta Kwankwaso, Ganduje Da Shekarau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dan takarar kujerar Sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyyar APC, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura, wanda aka fi sani da AA Zaura, ya bayyana kudirinsa na sasanta manyan ‘yan siyasar jihar guda uku wato Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Abdullahi Umar Ganduje da kuma Ibrahim Shekarau.

Zaura ya ce sulhun zai sauya yanayin siyasar Kano daga rigingimun ‘yan adawa zuwa siyasar ci gaba da za ta iya hanzarta ci gaba, kamar yadda ake gani a Legas da sauran jihohin da ke kan gaba.

  • Matsalar Wuta Ta Jefa Wasu Sassan Nijeriya Cikin Duhu
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara

Da yake jawabi yayin wani shirin siyasa da aka watsa a gidajen rediyon cikin gida, Zaura ya koka da cewa rarrabuwar kawuna a tsakanin ‘yan jam’iyyar na kawo cikas ga ci gaban Kano. Ya jaddada cewa dinke barakar da ke tsakaninsu shi ne mabudin bude kofa ga jihar.

“Siyasar adawa a Kano, kamar yadda ake bugawa a halin yanzu, ba ta da amfani. A shirye nake da in yi kokarin sasanta manyan shugabanninmu guda uku da suka hada da Kwankwaso, Ganduje da Shekarau. Kamata ya yi a saka Jihar Kano a gaba maimakon son zuciya. Idan har aka samu hakan, Legas da sauran jihohi za su zuba ido kan Kano domin samun darussa a harkokin siyasar ci gaba,” in ji shi.

Kokarin sulhunta Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na kasa, da kuma Kwankwaso, jagorar jam’iyyar NNPP na kasa, ya ci tura a baya saboda dambarwar siyasa. Yunkurin na karshe ya ci tura lokacin da magoya bayan Kwankwaso suka mara wa tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello baya domin ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa. A lokacin, Ganduje ya dage cewa shi uba ne ga duk wanda ke son shiga jam’iyyar APC, kalaman da ake ganin ya kawo cikas ga kokarin sulhu.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ba Zaura kadai ba ne yake kokarin ganin a samu zaman lafiya a tsakanin ‘yan siyasar guda ukun. Sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da suka hada da dan takarar mataimakin gwamnan jam’iyyar a zaben 2023, Murtala Sule Garo da kuma fitaccen dan siyasa, Baffa Babba Danagundi, sun yi irin wannan kira.

Kwankwaso, Ganduje, da Shekarau, wadanda dukkansu sun yi wa’adi biyu a matsayin gwamnan Kano, suna jam’iyyun siyasa daban-daban, kuma sun ci gaba da yin tasiri sosai a matakin kananan hukumomi, jiha, da kasa baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AA ZauraAPCKwankwasoShekarau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Darektan Jaridar The Guardian Ta Tanzaniya: Abubuwan Da Aka Tattauna a Manyan Taruka Biyu Na Sin Na Da Alaka Da Kasashen Duniya

Next Post

Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

LABARAI MASU NASABA

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.