• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karin magana na harshen Hausa su kan kunshi ma’ana mai zurfi. Misali “Kome nisan jifa, kasa zai fado.” Ana amfani da wannan karin magana wajen kwatanta yanayin farawar wani batu, da faduwarsa, gami da yadda ya kai karshe a wani yanayi da ba wanda zai iya magancewa. Kan haka ne nake dora alkalamina game da labarin da na ji na rufe hukumar taimaka wa aikin raya kasashe ta Amurka (USAID) a kwanakin baya, wanda nan take ya tuna min da wannan karin magana.

A cewar gwamnatin Amurka, hukumar USAID ta gaza tabbatar da cewa ayyukan da ta ba da kudin tallafi sun dace da muradun Amurka, bayan da ta shafe shekaru 64 tana aiki. Ban da haka, sakataren harkokin waje na kasar Amurka, Marco Rubio, ya ce hukumar ba ta cimma wani abu ba face kafa dimbin kungiyoyin da ba na gwamnati ba (NGO) a duk fadin duniya. Kana a wuraren da ta shiga, ba a cika cimma burin raya kasa ba, yayin da yanayin rashin kwanciyar hankali kan ta’azzara, kuma kyamar Amurka na kara yaduwa.

  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Sai dai kafin USAID ta fado kasa tamkar wani dutsen da kasar Amurka ta jefa, ta taba samun damar “tashi sama”, ma’ana cikin dogon lokaci hukumar ta zama daya daga cikin muhimman hukumomin da Amurka ke amfani da su wajen yin tasiri kan sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, inda hukumar ta samar da kudi da karfafa kungiyoyin NGO, da kafofin watsa labaru, da cibiyoyin bincike, da dai sauransu. Kana a cikin ayyukan da USAID ta yi, har da tallafa wa cibiyar bincike dake adawa da kasar Sin ta kasar Austiraliya (ASPI), domin ta kirkira da yada jita-jita game da Sin, da ba da tallafi ga kungiyoyin NGO da ‘yan adawa na kasashen Ukraine da Georgia don kitsa sauyin mulki a kasashen. Sa’an nan, a watan Fabrairun bana, wani dan majalisar dokokin Amurka ya ce hukumar USAID ta taba samar da kudi ga kungiyoyin ‘yan ta’adda irin su Al-Qaeda, da Boko Haram ta Najeriya.

Amma a hakika, ban da wadannan miyagun abubuwa da muka ambata, USAID ita ma ta ba da wasu gudummawa, musamman ta fuskar kiwon lafiya. Misali, wani rahoton bincike da mujallar kiwon lafiya ta Birtaniya “The Lancet” ta wallafa, ya yi hasashen cewa, raguwar kudin tallafin da aka samu sakamakon rufewar USAID, na iya haddasa mutuwar mutane fiye da miliyan 14 a duniya, ciki har da yara miliyan 4.5. Amma abin takaici shi ne, a ganin gwamnatin kasar Amurka ta yau, taimaka wa dorewar rayuwar mutane a kasashe masu tasowa “ba ta dace da muradun kasar Amurka ba”.

Hakika, da ma an san cewa tabbas Amurka za ta yi watsi da USAID. Saboda kasar ta kaddamar da shirin da zai samar da cikakken tasirinta a duniya a lokacin yakin cacar baka. Amma zuwa yanzu, tauraron kasar ya riga ya fara dishewa. Don haka ta yaya za ta samu isashen karfin cimma wani tsohon burinta da ta dade da sanyawa a rai? Idan an duba kudirin dokar “Babba kuma Kyakkyawa” (big and beautiful bill) da Amurka ta zartar kwanan nan, za a ga yadda kasar ta yi shirin rage kudin tallafin aikin jinya da na abinci, da sauran kudin tabbatar da jin dadin jama’a a cikin gidanta. Ta haka mun san cewa, ba za ta ci gaba da dora muhimmanci kan aikin jin kai a kasashen ketare ba.

Labarai Masu Nasaba

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Ta la’akari da wannan yanayin da kasar Amurka ke ciki, ma iya cewa, ita kanta ta zama kamar wani dutse ne da ke fadowa, kuma tabbas wata rana zai taba kasa! (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Next Post

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Related

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

3 days ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

3 days ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

7 days ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

1 week ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

1 week ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

July 26, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.