• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rashin ganin shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano a ziyarar ta’aziyya da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya kai ga iyalin Marigayin Alhaji Aminu Dantata, ya haifar da zazzafar muhawara a cikin jam’iyyar.

Rahotanni sun bayyana cewa yayin da jami’an gwamnatin Jihar Kano da ke cikin jam’iyyar NNPP suka yi tururuwan tarbar mataimakin shugaban kasan, ba a ga duriyar shugabannin jam’iyyar APC na jihar ba a wurin wannan taron da ya gudana a ranar Alhamis.

  • Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

Wannan lamari ya haifar da alamomin tambaya, yayin da wasu suna zargin cewa akwai rashi jituwa a cikin APC bayan saukar Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

Ganduje ya kasance tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda har yanzu ke da tasiri a cikin harkokin siyasar jihar, ya yi murabus daga mukamin shugaban APC a ranar 27 ga Yuni, sakamakon lissafin siyasa da shirye-shiryen da aka yi a cikin jam’iyyar kafin zaben 2027.

Masana harkokin siyasa suna ganin cewa wasu daga cikin shugabannin APC a jihar ba su yi farin ciki da murabus din Ganduje a matsayin shugaban APC na kasa ba, kuma suna ganin cewa Shettima ya taka rawa wajen tilasta wa Ganduje yin murabus.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Rahotanin sun bayyana cewa Shettima ya ziyarci Kano ne don yin ta’aziyyar rasuwar hamshakin dan kasuwa, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu kwanan nan, da kuma jajanta wa mutanen Kano kan wannan rashi.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa a irin wadannan manyan taruka a Nijeriya, an saba ganin shugabannin jam’iyya da goyon baya su tarbi manyan jami’ai kamar mataimakin shugaban kasa, amma lamarin ya bambanta yayin ziyarar Shettima, wanda ya haifar da zazzafar muhawara.

Da yake musanta cewa akwai rikice-rikice na cikin gida a jam’iyyar, sakataren APC a Kano, Ibrahim Zakari Sarina, ya shaida cewa rashin halartar shugabannin jam’iyyar a ziyarar ta’aziyya da mataimakin shugaban kasa ya kawo Kano ya faru ne sakamakon rashin sadarwa.

“Mun san cewa ziyarar za ta kasance, amma sadarwa ta zo a makare. Kafin mu shirya, mun riga mun makara. Saboda gwamnatin ta riga ta shirya tun kafin mu isa wurin.

“A gaskiya wannan abu ba ya da alaka da kowanne irin lamari na siyasa. An sanar da mu a makare, har ita kanta gwamnatin jihar a makare aka sanar da ita. Daga baya mun aike da godyarmu ga mataimakin shugaban kasa bisa ziyara, kuma ya fahimci yanayin sosai,” in ji Sarina.

Duk da wannan bayani, an samu rarrabuwan kai a tsakanin ‘yan siyasa a jihar.

Wani jigo a APC a yankin Gwale, Abdullahi Kabiru, ya bayyana cewa ya ji takaicin rashin halartar shugabannin jam’iyyar. “Wannan shi ne mataimakin shugaban kasa na wannan kasa, kuma ba mu kasa shirya tarba a gare shi ba? Wannan ba karamin kuskure ba ne. Ko da an samu rashin kyakkyawan sadarwa, yana nuna cewa akwai rashin hadin kai,” in ji shi.

Ita kuwa wata mai kishin jam’iyya, Amina Sani daga Tarauni, ra’ayinta ya sha bamban. Ta ce, “Na gamsu da bayanin da jam’iyyar ta bayar. Abubuwa suna faruwa a siyasa, musamman lokacin da jadawalin ke canzawa. Amma ina fatan hakan ba zai zama sabani ba. Dole ne mu girmama shugabanninmu da ofisoshinsu ba tare da la’akari da kowanne bambancin siyasa ba.”

Da yake jawabi kan lamarnin, wani masana harkokin siyasa, Dakta Musa Auwal ya bayyana cewa dole ne jam’iyyar ta yi taka-tsantsan. “Ko lamarin ya faru da gangan ko akasin haka, a duk lokacin da aka samu rarrabukan na manyan shugabannin jam’iyya a fili, yana rage karfin jam’iyyar kuma yana karfafa ‘yan adawa.

“APC a Kano tana taka muhimmiyar rawa a siyasan kasar nan, kuma kowanne takaddama da ke tasowa Kano na shugabancin ko na siyasa na iya zama babban lamari da ke daukan tsawon lokaci ana tattaunawa a kai,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCShettima
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Next Post

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

7 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.