• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

by Bello Hamza and Sulaiman
1 month ago
Dantsoho

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA ta bayyana cewa, a zango mai zuwa ne, za a fara aikin dala miliyan daya na Tashar Jirgen Ruwa da ke a jihar Legas.

 

A cewar Hukumar mai yuwa za a samu dan tsako kan ci gaba da aikin, saboda karancin manyan kayan aiki da za a yi aikin da su, a Tashar.

  • Tottenham Ta Ɗauki Xavi Simons Daga RB Leipzig
  • Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

Shugaban Hukumar ta NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ne, ya sanar da haka a wani taro hadaka a tsakanin Cibiyar kula da fitar da kaya ta kasa da Tashar Lekki da gudana a jihar Legas.

 

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Dantsoho ya sanar da cewa, tun lokacin da aka yi aikin Tashoshin Jiragen Ruwa na Tin Can Island shekaru 48 da kuma aikin Tashar Jiragen Ruwa ta and Apapa 103 a shekaru da suka gabata, babu wani yunkuri da aka yi, na gyransu ko kuma kara daga darajarsu.

 

Shugaban ya kuma koka kan yadda aka shafe wadannan shekarun masu yawan gaske, ba tare da an yi masu wani gyara ba.

 

Ya buga misali da kananan Tashoshin Jiragen Ruwa na kasasehe kamar na Togo, Côte d’Iboire da Ghana, wanda suka kasance, Tashoshin Jiragen Ruwa da manyan Jiragen Ruwa ke sauka.

A cewar Shugaban irin lalacewar da kayan aiki a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar suka yi, abu ne, da ya wuce kima, wanda hakan ya sanya, sauran Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma, har ta kai ga suna yin gasa na kasar nan, wajen gudanar da hada-hadar kasuwancinsu.

“Abokan gasar mu kamar Tashoshin Jiragen Ruwa na Lome, Cotonou, Abidjan da Tema, na yin amfani da damar halin da Tashoshin Jiragen mu suke a ciki ne, suke more damar gudanar da hada-hadarsu, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Shugaban.

“Dangane da bayaan da aka samu na duniya, Nijeriya ta kasance kasa, da ke da karfin tattalin ariziki kuma mai alumma da dama a fadin nahiyar Afirka, amma har zuwa yau, Abidjan da Lome na karbar saukar manyan Jiragen Ruwa masu yawa, fiye da wadanda suke sauka a Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas, “ Acewar Dantsoho.

Shugaban ya sanar da cewa, ya zama wajibi, mu tabbatar da mun ciki wannan gibin da ake da shi, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

Ya bayyana cewa, da zarar an samar da sauran kayan aikin da suka hada da kimiyyar zamani da sauransu, Tashoshin za a samu karin damar saukar manyan Jiragen Ruwan.

Ya kuma koka kan karancin kayan aiki na saukar Jiragen a Tashoshin, wanda hakan ya sanya, Hukumar ta NPA ke zuba sabbin kayan aikin ciki har da manyan motocin janyewa da sauransu.

Sai dai, ya sanar da a zagon farko na shekarar 2026 ake sa ran isowar kayan zuwa cikin kasar nan

Ya ci gaba da cewa, hakan ne ke shafar Matatar Mai ta Dangote da ke a Lekki inda ya yi nuni da cewa, Hukumar ta NPA kuma, ba ta irin kayan aikin da za su iya janyo wadannan Tankokin Man din.

Dantsoho ya sanar da cewa, Gwamnatin Tarayya ta kafa wani waje domin samar da saukin gudanar da ayyukan Matatar Mai ta Dangote, inda aka warewa hukumomin Gwamnati guda 16 wasu gurare, a cikin harabar Hukumar NPA, wanda hakan ya bai wa NPA damar tara kudaden shiga da suka kai sama da Naira biliyan 25, tun daga watan Okutobar 2024, zuwa yau.

Ya ce, NPA na goyon bayan sauye-sauyen da Gwamnatin ke ci gaba da yi, a fannin tattalin arzikin kasar, wanda hakjan zai janyo hankulan masu son zuba hannun jari a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar

Shi kuwa Aminu Umar, Shugaban Cibiyar a jawabinsa na maraba a wajen taron ya jaddada cewa, kirkiro da Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na Teku, hakan na da matukar mahimmanci a bangaren shigo da kaya daga waje da kuma fitar da su, daga cikin kasar zuwa ketare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi
Tattalin Arziki

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Next Post
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Dantsoho

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.