ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

by Bello Hamza and Sulaiman
11 months ago
Dantsoho

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA ta bayyana cewa, a zango mai zuwa ne, za a fara aikin dala miliyan daya na Tashar Jirgen Ruwa da ke a jihar Legas.

 

A cewar Hukumar mai yuwa za a samu dan tsako kan ci gaba da aikin, saboda karancin manyan kayan aiki da za a yi aikin da su, a Tashar.

ADVERTISEMENT
  • Tottenham Ta Ɗauki Xavi Simons Daga RB Leipzig
  • Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

Shugaban Hukumar ta NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ne, ya sanar da haka a wani taro hadaka a tsakanin Cibiyar kula da fitar da kaya ta kasa da Tashar Lekki da gudana a jihar Legas.

 

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Dantsoho ya sanar da cewa, tun lokacin da aka yi aikin Tashoshin Jiragen Ruwa na Tin Can Island shekaru 48 da kuma aikin Tashar Jiragen Ruwa ta and Apapa 103 a shekaru da suka gabata, babu wani yunkuri da aka yi, na gyransu ko kuma kara daga darajarsu.

 

Shugaban ya kuma koka kan yadda aka shafe wadannan shekarun masu yawan gaske, ba tare da an yi masu wani gyara ba.

 

Ya buga misali da kananan Tashoshin Jiragen Ruwa na kasasehe kamar na Togo, Côte d’Iboire da Ghana, wanda suka kasance, Tashoshin Jiragen Ruwa da manyan Jiragen Ruwa ke sauka.

A cewar Shugaban irin lalacewar da kayan aiki a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar suka yi, abu ne, da ya wuce kima, wanda hakan ya sanya, sauran Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma, har ta kai ga suna yin gasa na kasar nan, wajen gudanar da hada-hadar kasuwancinsu.

“Abokan gasar mu kamar Tashoshin Jiragen Ruwa na Lome, Cotonou, Abidjan da Tema, na yin amfani da damar halin da Tashoshin Jiragen mu suke a ciki ne, suke more damar gudanar da hada-hadarsu, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Shugaban.

“Dangane da bayaan da aka samu na duniya, Nijeriya ta kasance kasa, da ke da karfin tattalin ariziki kuma mai alumma da dama a fadin nahiyar Afirka, amma har zuwa yau, Abidjan da Lome na karbar saukar manyan Jiragen Ruwa masu yawa, fiye da wadanda suke sauka a Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas, “ Acewar Dantsoho.

Shugaban ya sanar da cewa, ya zama wajibi, mu tabbatar da mun ciki wannan gibin da ake da shi, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

Ya bayyana cewa, da zarar an samar da sauran kayan aikin da suka hada da kimiyyar zamani da sauransu, Tashoshin za a samu karin damar saukar manyan Jiragen Ruwan.

Ya kuma koka kan karancin kayan aiki na saukar Jiragen a Tashoshin, wanda hakan ya sanya, Hukumar ta NPA ke zuba sabbin kayan aikin ciki har da manyan motocin janyewa da sauransu.

Sai dai, ya sanar da a zagon farko na shekarar 2026 ake sa ran isowar kayan zuwa cikin kasar nan

Ya ci gaba da cewa, hakan ne ke shafar Matatar Mai ta Dangote da ke a Lekki inda ya yi nuni da cewa, Hukumar ta NPA kuma, ba ta irin kayan aikin da za su iya janyo wadannan Tankokin Man din.

Dantsoho ya sanar da cewa, Gwamnatin Tarayya ta kafa wani waje domin samar da saukin gudanar da ayyukan Matatar Mai ta Dangote, inda aka warewa hukumomin Gwamnati guda 16 wasu gurare, a cikin harabar Hukumar NPA, wanda hakan ya bai wa NPA damar tara kudaden shiga da suka kai sama da Naira biliyan 25, tun daga watan Okutobar 2024, zuwa yau.

Ya ce, NPA na goyon bayan sauye-sauyen da Gwamnatin ke ci gaba da yi, a fannin tattalin arzikin kasar, wanda hakjan zai janyo hankulan masu son zuba hannun jari a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar

Shi kuwa Aminu Umar, Shugaban Cibiyar a jawabinsa na maraba a wajen taron ya jaddada cewa, kirkiro da Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na Teku, hakan na da matukar mahimmanci a bangaren shigo da kaya daga waje da kuma fitar da su, daga cikin kasar zuwa ketare.

Dantsoho
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
Dantsoho
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.