ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

by Bello Hamza and Sulaiman
10 months ago
Dantsoho

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA ta bayyana cewa, a zango mai zuwa ne, za a fara aikin dala miliyan daya na Tashar Jirgen Ruwa da ke a jihar Legas.

 

A cewar Hukumar mai yuwa za a samu dan tsako kan ci gaba da aikin, saboda karancin manyan kayan aiki da za a yi aikin da su, a Tashar.

ADVERTISEMENT
  • Tottenham Ta Ɗauki Xavi Simons Daga RB Leipzig
  • Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

Shugaban Hukumar ta NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ne, ya sanar da haka a wani taro hadaka a tsakanin Cibiyar kula da fitar da kaya ta kasa da Tashar Lekki da gudana a jihar Legas.

 

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Dantsoho ya sanar da cewa, tun lokacin da aka yi aikin Tashoshin Jiragen Ruwa na Tin Can Island shekaru 48 da kuma aikin Tashar Jiragen Ruwa ta and Apapa 103 a shekaru da suka gabata, babu wani yunkuri da aka yi, na gyransu ko kuma kara daga darajarsu.

 

Shugaban ya kuma koka kan yadda aka shafe wadannan shekarun masu yawan gaske, ba tare da an yi masu wani gyara ba.

 

Ya buga misali da kananan Tashoshin Jiragen Ruwa na kasasehe kamar na Togo, Côte d’Iboire da Ghana, wanda suka kasance, Tashoshin Jiragen Ruwa da manyan Jiragen Ruwa ke sauka.

A cewar Shugaban irin lalacewar da kayan aiki a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar suka yi, abu ne, da ya wuce kima, wanda hakan ya sanya, sauran Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma, har ta kai ga suna yin gasa na kasar nan, wajen gudanar da hada-hadar kasuwancinsu.

“Abokan gasar mu kamar Tashoshin Jiragen Ruwa na Lome, Cotonou, Abidjan da Tema, na yin amfani da damar halin da Tashoshin Jiragen mu suke a ciki ne, suke more damar gudanar da hada-hadarsu, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Shugaban.

“Dangane da bayaan da aka samu na duniya, Nijeriya ta kasance kasa, da ke da karfin tattalin ariziki kuma mai alumma da dama a fadin nahiyar Afirka, amma har zuwa yau, Abidjan da Lome na karbar saukar manyan Jiragen Ruwa masu yawa, fiye da wadanda suke sauka a Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas, “ Acewar Dantsoho.

Shugaban ya sanar da cewa, ya zama wajibi, mu tabbatar da mun ciki wannan gibin da ake da shi, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

Ya bayyana cewa, da zarar an samar da sauran kayan aikin da suka hada da kimiyyar zamani da sauransu, Tashoshin za a samu karin damar saukar manyan Jiragen Ruwan.

Ya kuma koka kan karancin kayan aiki na saukar Jiragen a Tashoshin, wanda hakan ya sanya, Hukumar ta NPA ke zuba sabbin kayan aikin ciki har da manyan motocin janyewa da sauransu.

Sai dai, ya sanar da a zagon farko na shekarar 2026 ake sa ran isowar kayan zuwa cikin kasar nan

Ya ci gaba da cewa, hakan ne ke shafar Matatar Mai ta Dangote da ke a Lekki inda ya yi nuni da cewa, Hukumar ta NPA kuma, ba ta irin kayan aikin da za su iya janyo wadannan Tankokin Man din.

Dantsoho ya sanar da cewa, Gwamnatin Tarayya ta kafa wani waje domin samar da saukin gudanar da ayyukan Matatar Mai ta Dangote, inda aka warewa hukumomin Gwamnati guda 16 wasu gurare, a cikin harabar Hukumar NPA, wanda hakan ya bai wa NPA damar tara kudaden shiga da suka kai sama da Naira biliyan 25, tun daga watan Okutobar 2024, zuwa yau.

Ya ce, NPA na goyon bayan sauye-sauyen da Gwamnatin ke ci gaba da yi, a fannin tattalin arzikin kasar, wanda hakjan zai janyo hankulan masu son zuba hannun jari a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar

Shi kuwa Aminu Umar, Shugaban Cibiyar a jawabinsa na maraba a wajen taron ya jaddada cewa, kirkiro da Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na Teku, hakan na da matukar mahimmanci a bangaren shigo da kaya daga waje da kuma fitar da su, daga cikin kasar zuwa ketare.

Dantsoho
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Dantsoho
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Sulaiman
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Sulaiman
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Sulaiman
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.