Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home ADABI

ADABI: Asalin Rubu-tun Hausar Boko Da Bunkasar Harshen Hausa

by Tayo Adelaja
September 24, 2017
in ADABI
5 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

DAGA SADIK TUKUR GWARZO

Cigaba daga makon jiya

samndaads

Bayan kura ta lafa, sai Gwamna Luggard ya tura sako ga kasarsu Ingila a rohoton da ya ke turawa lokaci zuwa lokaci gami da labarta mu su abinda ya sami Kyaftin Moloney. Shi ne har ya ke fada mu su cewa, ba lallai ne a ce tafintan Kyaftin Moloney da gayya ya yi wannan kasassabar ba, sai dai watakila hakan ta faru ne, saboda rashin samun wata fahimta da Kyaftin Moleney ya yi dangane da yaren Hausa ta yadda har ya kasa tantance tsakanin abinda ya ke karantawa da abinda tafintansa ya ke fada.

Don haka a karshe Luggard ya bada shawarar cewa a ganinsa mafitar kare aukuwar irin wannan hadari a nan gaba shi ne Turawan mulki ’yan uwansa su koyi Hausa. Wannan ya na cikin D.J.M Muffet, concerning Brabe Captain, London 1964.

Rubutun Boko Na Farko

Sai dai abu ne mai matukar wuya a gane wanda ya fara rubuta Hausa da haruffan Romawa (Rubutun Boko) kasancewar bauta da kasuwanci sun sanya Hausawa shiga kasashen Larabawa lokaci mai tsawo da ya gabata. Daga can kuma an tsallaka da wasu izuwa yankunan Turai da sauran sassan duniya masu nisan gaske duk da zummar yin bauta.

Kowa ya san an yi zamunna na cinikin bayi a baya, sannan shaharar masautar Borno ba karamar aba ba ce. Ita ce a ka ce sarakunanta sun shahara har ma a ka ce a wajajen karni na 11 su ka fara hurda da Larabawa, sannan kuma idan yakinsu ya motsa, mamaya su ke kawowa dukkanin makwabtan kasashe, ciki kuwa harda kasar Hausa.

An ce, tun zamani mai tsawo da su ka gabata akwai Hausawa masu yin bauta a Turabulus da makwabtan kasashe, wadanda a ke kyautata zaton daga Borno a ka kwashe su izuwa can.

Ta na iya kasancewa wani daga Turawa ko Girkawa ya taba jarraba amsar labaru daga wani Bahaushe gami da rubuta shi da Romanci (Boko), amma abin bai fito ga duniya har mun riske shi ba. Amma dai mafi dadewar rubutun Boko da a ka samu shi ne wanda Marubuci Ibrahim Yaro Yahaya (Allah Ya ji kansa da rahama) ya kawo a shafi na 74 na littafinsa mai suna ‘Hausa A Rubuce.’ inda ya ke cewa, “Watakila za a yi mamaki a ji cewa a kasar Denmark ta Turai a ka fara samun an rubuta kalmomin Hausa a cikin rubutun Boko tun a karni na 18.

Yadda abin ya faru shi ne a cikin shekarar 1772 sarkin Denmark ya tura wakilansa izuwa Arabiya, don gudanar da bincike na kimiyya. A cikin wakilan har da wani mai suna B.G Neibuhr, wanda shi ne kadai ya tsira kuma har ya koma gida kasarsa.

To, a wannan shekarar sai wani Balaraben Tunis ya je Denmark ziyara. Sunansa Abdurrahman. A tare da shi akwai wani bawansa Bahaushe. Sai sarkin Denmark ya sa a ka kira Niebuhr, domin ya zama tafinta tsakaninsa da Balaraben nan, kasancewar shi Niebuhr ya koyi Larabci a tafiyar da yayi izuwa Arebiya.

Ga wasu kalmomi da a ka samu Niebuhr ya rubuta a Hausar Boko, kamar yadda ya ji daga bakin wannan bawa Bahaushe.

Dudsji – Dutse

Ghaui – Gari

Dsjenari – Zinari

Ghurasa – Gurasa

Crua – Ruwa

Sirki – Sarki

Schensali – Shaidani

Berni – Birni

Na baya daga wannan kuma shi ne rubuce-rubucen da Baturen Mishan mai suna J.F Schon ya yi da Hausa a wuraren 1856 lokacin da ya roki Dr. Barth ya ba shi aron yaransa biyu, Dorugu da Abega, don su taimaka ma sa wajen yin rubututtukan Hausa.

A wancan lokacin ne Dorugu ya rika fadar labarun Hausa, shi kuma ya na rubutawa, har a ka samu cewa J. F Schon din ya rubuta litttattafai. Misalin magana Hausa, Littafin Musa na fari, Labari Nagari, Dictionary of the Hausa da sauransu.

Saboda a shekarar 1900 AD ne gwamnatin Ingila ta karbe ragamar mulki daga hannun sarakunan Hausawa, amma sai a 1903 sojojin Gwamna Luggard su ka cinye Kano da Sakkwato a yaki, sannan su ka bude makaranta ta farko a Sokoto tare da malamai biyu, watau Mr. Kurdan da mataimakinsa Malam Ibrahim, amma makarantar ba ta dade ba, saboda iyaye sun ki sanya ‘ya’yansu, don gudun kada a cusa mu su akidar Kiristanci.

Farfesa ya nuna cewa rashin gamsuwar Hausawa ga ilimin da Turawa su ke shirin ba su dadadden abu ne, kuma tun a wancan zamanin kalmar ‘Boko’ ta samo asali wadda a cewarsa ma’anar ta da Hausa shi ne kamar a ce ‘rufe kura da fatar akuya’ (watau a yi basaja wajen rufe wani abu da wani abu).

Tun kafin wannan ma, shi kanshi Luggard sai da ya kalli Hausawa da yadda su ka yi riko da addini tun a lokacin, sannan ya yi amannar cewa bai yiwuwa a ce za a koyar da su Boko kamar yadda a ke koyar da shi a kasarsu Ingila.

A wani zancen kuma, cewa a ka yi tun sa’ar da Luggard ya ke yaki a kasar nan ya fara sanyawa a na rubuta Hausa ta hanyar amfani da rubutun Romawa (Boko). Saboda kamar yadda mu ka fada tun a baya Lugga ya fahimci tasiri da bunkasar yaren Hausa a wannan yanki na Arewa, amma kuma a wurinsa bai yiwuwa ya rubuta Hausa da ajami kamar yadda ya samu Hausawan lokacin su na yi.

SendShareTweetShare
Previous Post

ADABI: Mene Ne Adabin Kasuwa? (II)

Next Post

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Maida Masaukin Shugaban Kasa Makaranta

RelatedPosts

Fitattun Littattafan Hausa A 2020

Fitattun Littattafan Hausa A 2020

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Masu iya magana suka ce 'komai ya yi farko zai...

Rayuwan Aurena

Sharhin Littafin: A Rayuwar Aurena: Abin Da Ba Zan Manta Da Shi Ba

by Muhammad
2 weeks ago
0

Na Adamun Adamawa Bauchi Daga Yusuf Kabir 09063281016 Sunan wannan...

Zama Farfesa

Ina Son Zama Farfesa, Cewar ’Yar Shekara 18 Da Ta Wallafa Littafi A Kebbi

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

MAIMUNA GARBA HAMMANI wata matsashiyyar yarinya ce ’yar Shekaru 18...

Next Post

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Maida Masaukin Shugaban Kasa Makaranta

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version