Ambaliyar ruwan da ta faru a Jihar Neja ranar Alhamis ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 115, inda fiye da gidaje 300 suka lalace. Rahotanni daga Hukumar taimakon gaggawa ta Jihar, sun tabbatar da cewa adadin mutanen da suka rasa rayuka ya tashi daga asalin 20 zuwa 115. Hukumar ta kuma bayyana cewa har yanzu ana gudanar da ayyukan ceto domin gano sauran waɗanda ba a samu bayanai daga gare su ba.
Shugaban Hukumar, Abdullahi Baba Arah, ya sanar da wakilinmu cewa an samu ƙarin gawarwaki ranar Jumma’a, wanda ya nuna cewa ambaliyar ta shafi garin Mokwa da sauran yankuna na ƙaramar hukumar Mokwa. Arah ya kuma tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike da taimakon waɗanda ambaliyar ta shafa, amma wasu daga cikin mutanen da aka rasa ba’a gansu ba.
- Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
- Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
Mazauna yankin sun bayyana cewa ambaliyar ta shafi dukan al’umma, inda wasu iyalai suka rasa dukkannin ‘ya’yansu. Wata mata mai suna Kaka Dazana ta rasa dukkan ‘ya’yanta huɗu, yayin da wani a iyali guda ya rasa mutum 13 daga cikin 15. Haka kuma, wata mata tare da ‘ya’yanta guda uku sun ɓace, ba tare da wata alamar samunsu a raye ba.
Rahotanni daga shaidu sun bayyana cewa wasu daga cikin matafiya da suka tsaya a garin Mokwa don yin addu’a ko kuma tsayawa don su kwana, sun shiga cikin ambaliyar, amma ba a samu bayanai game da su ba. Makarantu da masallatai na yankin sun nutse cikin ruwa, wanda ya ƙara tabarbarewar al’amuran.
Gwamnatin Jihar Nijar na ci gaba da gudanar da ayyukan ceto da kuma samar da tallafi ga waɗanda abin ya shafa, yayin da ake ci gaba da bincike. Ahalin yanzu, akwai matuƙar damuwa daga al’ummar garin Mokwa da sauran yankunan da ambaliyar ta shafa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp