ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu

Mun wallafa a 27 ga Janairu, 2023

by Leadership Hausa
2 years ago
Kano

FARFESA HABU MUHAMMAD, fitacce ne a Jami’ar Bayero da ma sauran jami’oin gida da na waje, mutun ne mai kishin ganin an inganta tsarin Dimokuradiyya, da kyakkyawan shugabanci a Nijeriya baya ga zamowar sa cikin masu kyakyawar fahimta a kan al’adu da harshen Hausa. Watanni biyu da suka gabata, ya zama shugaban cibiyyar nazarin kimiyyar siyasa da ke gidan tunawa da marigayi Malam Aminu Kano, wanda aka fi sani da Gidan Mumbayya da ke karkashin Jami’ar Bayero ta Kano. Wakilinmu MUSTAPA IBRAHIM KANO ya tattauna da shi kan akidar siyasar Malam Aminu Kano, daya daga cikin mazan jiya ‘yan gwagwarmaya, da kuma ta ‘yan siyasar wannan zamanin. Har ila yau da sauran wasu al’amura da aka bullo da su a cibiyar wanda za a rika gabatarwa da harshen Hausa zalla, ga dai tattaunawar kamar haka:

Da farko za mu so ka gabatar da kanka…

Sunana Farfesa Habu Muhammad, ni ne Babban Darakta ko kuma in ce, Shugaban Cibiyar Nazarin Kimiyyar Siyasa, da ke Gidan tunawa da Malam Aminu Kano, wato Gidan Mumbayya, da ke karkashin Jami’ar Bayero ta Kano. Na zama Daraktan wannan cibiya ne a ranar 6 ga Oktoban 2022. Hakan ta kasance ne bayan mutumin da na gada Farfesa Zango ya kammala wa’adin aikinsa na jagorancin gidan da ke Unguwar Gwammaja, a Karamar Hukumar Dala.

ADVERTISEMENT

Farfesa bari mu dan yi waiwaye adon tafiya, ko za ka dora akidar siyasar Malam Aminu Kano da ta ‘yan siyasar yau a mizani?

To ita siyasa irin ta su Malam Aminu Kano siyasa ce ta a kida ta a `yantar da talaka daga kangin bauta da wulakanci da ake wa talaka a wancan lokacin, kuma siyasa ce ta neman `yanci domin sun san, ko mene ne ‘yanci domin ko ba komai sun yi gwagwarmaya da gumurzu na shan wahala da suka samu daga turawan mulkin mallaka kan maganar `yanci. To ka ga wasu daga cinkin su ko su Malam Aminu Kano suna da wannann ilimin kuma suna da wannan ruhin na neman `yanci cikin wahala da azaba da matsaloli daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Saboda haka za ka ga siyasar su Malam Aminu Kano siyasa ce ta neman `yancin talaka, da `yantar da shi daga kangin bauta da za ka iya cewa masu gudanar da mulki na wancan lokacin sun sa talaka a kangin bauta, haka ne ma ya sa su Malam Aminu Kano da sauran `yan siyasar zamaninsa suke da wani take na SAWABA-SAWABA, to abin da suke nufi a wancan lokacin nasu shi ne irin abin da suke wa talaka na karbar haraji, da jangali, da sa mutum noma a gonar Rogo, ko makamancin haka ba tare da an biya shi ba, to wannan da wasu abu masu kama da wannan shi ne abin da su Malam Aminu Kano suka yi yaki da shi a tafiyarsu ta NEPU da PRP kuma wannan za ka ga cewa ita ce a kidar su Malam Aminu Kano da sauransu.

Kuma har ila yau wani abin lura, su, su Malam Aminu Kano babu batun tara kudi a akidar su illa dai kawai `yancin talaka, da biya masa bukata daidai gwargwadon iko, ka ga babu maganar cin hanci da rashawa da almundahana amma na yanzu mafiyawa daga cikinsu ko 99 bisa 100 suna kokarin tara abin duniya ne har ma ya fi karfin bukatarsu ta rayuwa. To saboda haka a takaice akidar siyasar Malam Aminu Kano ta sha bamban nesa ba kusa ba da `yan siyasarmu na yau.

Bambanci ko kuma in ka kwatanta da `yan siyasar yanzu a kasin haka ne, wato su ‘yan siyasar yanzu ba su san ma mene ne `yanci ba, abin da suka sani shi ne tara kudi dan amfanin kansu da `ya`yansu, da matansu, da wadanda suke so su azurta, saboda haka idan ka kwatanta siyasar su Malam Aminu Kano da `yan siyasar yau abin ya sha bamban nesa ba kusa ba saboda canjin zamani da canjin yanayin.

Farfesa, wacce rawa jaridun Hausa za su taka wajen samun nasarar wadannan sabbin tsare-tsare?

To bisa la’akari da yadda muka lura da cewa kafofin yada labarai na Hausa da jaridun Hausa suna da dinbim makaranta da masu bibiyarsu babu shakka, haka za mu hada kai da Jaridun Hausa sosai domin isar da sako a lungu na birni da karkara, ba ma kamar mutanenmu da suke kudancin kasar nan da ma sauran wasu wurare suna bibiyar jaridun Hausa da sauransu. Yanzu ana bibiyarmu ma ta hanyar kafofin sadarwa na zamani, to wannan abu ne da za mu yi iya kokarinmu mu ga mun hada kai da duk wata kafa da sakonmu zai isa duk inda ake bukata gwargwadon hali.

Ana yin hakan ne domin al’umma  su rika samu  suna karantawa a kokarin da muke na wayar da kan al’umma ta kowanne fanni, har ma da abubuwan da suka shafi turanci shi ma sai an yi  da shi, duk da yake mu dai burinmu shi ne masu jin Hausa a ba su damarsu ta karantawa da Hausa da kuma saurare da sauransu, burinmu dai shi ne mu ilmantar da al’umma masu jin Turanci da masu jin Hausa zalla, a wannan cibiya ta nazarin kimiyyar siyasa ta Gidan Mumbayya.

Haka nan muna da dangantaka ko alaka kyakkyawa da kafofin yada labarai na Talbijin, da Rediyo dake nan Kano da muke gabatar da shirye-shirye, a kullum so ake a fadi wani abu domin yada ilimi cikin duniya ta wadanan kafofi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina - Sarkin Kagarko

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.