• English
  • Business News
Sunday, May 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu

Mun wallafa a 27 ga Janairu, 2023

by Leadership Hausa
1 year ago
in Rahotonni
0
Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

FARFESA HABU MUHAMMAD, fitacce ne a Jami’ar Bayero da ma sauran jami’oin gida da na waje, mutun ne mai kishin ganin an inganta tsarin Dimokuradiyya, da kyakkyawan shugabanci a Nijeriya baya ga zamowar sa cikin masu kyakyawar fahimta a kan al’adu da harshen Hausa. Watanni biyu da suka gabata, ya zama shugaban cibiyyar nazarin kimiyyar siyasa da ke gidan tunawa da marigayi Malam Aminu Kano, wanda aka fi sani da Gidan Mumbayya da ke karkashin Jami’ar Bayero ta Kano. Wakilinmu MUSTAPA IBRAHIM KANO ya tattauna da shi kan akidar siyasar Malam Aminu Kano, daya daga cikin mazan jiya ‘yan gwagwarmaya, da kuma ta ‘yan siyasar wannan zamanin. Har ila yau da sauran wasu al’amura da aka bullo da su a cibiyar wanda za a rika gabatarwa da harshen Hausa zalla, ga dai tattaunawar kamar haka:

Da farko za mu so ka gabatar da kanka…

Sunana Farfesa Habu Muhammad, ni ne Babban Darakta ko kuma in ce, Shugaban Cibiyar Nazarin Kimiyyar Siyasa, da ke Gidan tunawa da Malam Aminu Kano, wato Gidan Mumbayya, da ke karkashin Jami’ar Bayero ta Kano. Na zama Daraktan wannan cibiya ne a ranar 6 ga Oktoban 2022. Hakan ta kasance ne bayan mutumin da na gada Farfesa Zango ya kammala wa’adin aikinsa na jagorancin gidan da ke Unguwar Gwammaja, a Karamar Hukumar Dala.

Farfesa bari mu dan yi waiwaye adon tafiya, ko za ka dora akidar siyasar Malam Aminu Kano da ta ‘yan siyasar yau a mizani?

To ita siyasa irin ta su Malam Aminu Kano siyasa ce ta a kida ta a `yantar da talaka daga kangin bauta da wulakanci da ake wa talaka a wancan lokacin, kuma siyasa ce ta neman `yanci domin sun san, ko mene ne ‘yanci domin ko ba komai sun yi gwagwarmaya da gumurzu na shan wahala da suka samu daga turawan mulkin mallaka kan maganar `yanci. To ka ga wasu daga cinkin su ko su Malam Aminu Kano suna da wannann ilimin kuma suna da wannan ruhin na neman `yanci cikin wahala da azaba da matsaloli daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Saboda haka za ka ga siyasar su Malam Aminu Kano siyasa ce ta neman `yancin talaka, da `yantar da shi daga kangin bauta da za ka iya cewa masu gudanar da mulki na wancan lokacin sun sa talaka a kangin bauta, haka ne ma ya sa su Malam Aminu Kano da sauran `yan siyasar zamaninsa suke da wani take na SAWABA-SAWABA, to abin da suke nufi a wancan lokacin nasu shi ne irin abin da suke wa talaka na karbar haraji, da jangali, da sa mutum noma a gonar Rogo, ko makamancin haka ba tare da an biya shi ba, to wannan da wasu abu masu kama da wannan shi ne abin da su Malam Aminu Kano suka yi yaki da shi a tafiyarsu ta NEPU da PRP kuma wannan za ka ga cewa ita ce a kidar su Malam Aminu Kano da sauransu.

Kuma har ila yau wani abin lura, su, su Malam Aminu Kano babu batun tara kudi a akidar su illa dai kawai `yancin talaka, da biya masa bukata daidai gwargwadon iko, ka ga babu maganar cin hanci da rashawa da almundahana amma na yanzu mafiyawa daga cikinsu ko 99 bisa 100 suna kokarin tara abin duniya ne har ma ya fi karfin bukatarsu ta rayuwa. To saboda haka a takaice akidar siyasar Malam Aminu Kano ta sha bamban nesa ba kusa ba da `yan siyasarmu na yau.

Bambanci ko kuma in ka kwatanta da `yan siyasar yanzu a kasin haka ne, wato su ‘yan siyasar yanzu ba su san ma mene ne `yanci ba, abin da suka sani shi ne tara kudi dan amfanin kansu da `ya`yansu, da matansu, da wadanda suke so su azurta, saboda haka idan ka kwatanta siyasar su Malam Aminu Kano da `yan siyasar yau abin ya sha bamban nesa ba kusa ba saboda canjin zamani da canjin yanayin.

Farfesa, wacce rawa jaridun Hausa za su taka wajen samun nasarar wadannan sabbin tsare-tsare?

To bisa la’akari da yadda muka lura da cewa kafofin yada labarai na Hausa da jaridun Hausa suna da dinbim makaranta da masu bibiyarsu babu shakka, haka za mu hada kai da Jaridun Hausa sosai domin isar da sako a lungu na birni da karkara, ba ma kamar mutanenmu da suke kudancin kasar nan da ma sauran wasu wurare suna bibiyar jaridun Hausa da sauransu. Yanzu ana bibiyarmu ma ta hanyar kafofin sadarwa na zamani, to wannan abu ne da za mu yi iya kokarinmu mu ga mun hada kai da duk wata kafa da sakonmu zai isa duk inda ake bukata gwargwadon hali.

Ana yin hakan ne domin al’umma  su rika samu  suna karantawa a kokarin da muke na wayar da kan al’umma ta kowanne fanni, har ma da abubuwan da suka shafi turanci shi ma sai an yi  da shi, duk da yake mu dai burinmu shi ne masu jin Hausa a ba su damarsu ta karantawa da Hausa da kuma saurare da sauransu, burinmu dai shi ne mu ilmantar da al’umma masu jin Turanci da masu jin Hausa zalla, a wannan cibiya ta nazarin kimiyyar siyasa ta Gidan Mumbayya.

Haka nan muna da dangantaka ko alaka kyakkyawa da kafofin yada labarai na Talbijin, da Rediyo dake nan Kano da muke gabatar da shirye-shirye, a kullum so ake a fadi wani abu domin yada ilimi cikin duniya ta wadanan kafofi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Rahotanninmu Na Musamman A 2023: Asalin Garkin Abuja Da Ya Shafe Sama Da Shekara 177 Da Kafuwa

Next Post

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina - Sarkin Kagarko

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

May 17, 2025
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

May 17, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 17, 2025
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

May 17, 2025
Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

May 17, 2025
Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

May 17, 2025
Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

May 17, 2025
Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

May 17, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

May 17, 2025
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.