• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Majalisar Kano Ta Nemi Taimakon Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kai dauki ga al’ummar da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.

‘Yan majalisar sun yi wannan kiran ne a zaman da suka yi a ranar Litinin, wanda shugaban majalisar, Hamisu Chidari ya jagoranta.

  • Bikin Tsakiyar Kaka Na 2022 Da CMG Ya Nuna Ya Samu Yabo Sosai Daga Masu Kallo A Gida Da Waje
  • Kashi 78 Na Dalibai Sun Ci Jarrabawar NBAIS Ta 2022 – Farfesa Shafi’u

Majalisar ta yi wannan kiran ne bayan gabatar da kudiri kan al’amuran hadin gwiwa da suka shafi rayuwar jama’a cikin gaggawa da ‘yan mazabar Kiru, Bebeji da Rano suka gabatar.

Mataimakin shugaban majalisar kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Kiru, Kabiru Dashi ne, ya gabatar wa da majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi kira ga hukumar raya kogin Hadejia da Jama’are da gwamnatin tarayya da su gaggauta magance kwararar ruwa daga madatsar ruwa ta Tiga.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

A cewarsu, yin hakan zai kawo karshen matsalar ambaliyar ruwa da asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

‘Yan majalisar sun bayyana lamarin a matsayin abin takaici da bakin ciki, yayin da suka kuma yi kira ga gwamnatin jihar Kano da gwamnatin tarayya da su kawo dauki ga al’umma.

Bayan tattaunawa ne majalisar ta amince da kudirorin, inda ta jajanta wa al’ummar da abin ya shafa tare da addu’ar Allah ya kare afkuwar wannan lamari.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa ambaliyar ruwa ta Tiga a makon jiya ta yi barna tare da lalata gonaki da tituna da gidaje da kuma raba mazauna yankunan da muhallansu.

A halin da ake ciki, majalisar ta samu takarda daga gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje na neman amincewar nadin shugaban majalisar tare da sake nada wasu mutane biyar na kwamitin gyaran doka na jihar.

Hukumar Gyaran Shari’a ta kunshi Mai Shari’a Lawan Wada mai ritaya a matsayin shugaba, sai Sadiq Garba, Muhd, Aliyu, Yahaya Rimi, Dakta Muhammad Minjibir, Garzali Zubairu da Hauwa Yusuf a matsayin mambobi.

Wasikar dai an mika ta ne ga kwamitin shari’a na majalisar kuma an ba shi mako guda ya ba da rahoto don ci gaba da ayyukan majalisa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace Fasto A Filato

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.