• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Majalisar Kano Ta Nemi Taimakon Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Majalisar Kano Ta Nemi Taimakon Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kai dauki ga al’ummar da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.

‘Yan majalisar sun yi wannan kiran ne a zaman da suka yi a ranar Litinin, wanda shugaban majalisar, Hamisu Chidari ya jagoranta.

  • Bikin Tsakiyar Kaka Na 2022 Da CMG Ya Nuna Ya Samu Yabo Sosai Daga Masu Kallo A Gida Da Waje
  • Kashi 78 Na Dalibai Sun Ci Jarrabawar NBAIS Ta 2022 – Farfesa Shafi’u

Majalisar ta yi wannan kiran ne bayan gabatar da kudiri kan al’amuran hadin gwiwa da suka shafi rayuwar jama’a cikin gaggawa da ‘yan mazabar Kiru, Bebeji da Rano suka gabatar.

Mataimakin shugaban majalisar kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Kiru, Kabiru Dashi ne, ya gabatar wa da majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi kira ga hukumar raya kogin Hadejia da Jama’are da gwamnatin tarayya da su gaggauta magance kwararar ruwa daga madatsar ruwa ta Tiga.

Labarai Masu Nasaba

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

A cewarsu, yin hakan zai kawo karshen matsalar ambaliyar ruwa da asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

‘Yan majalisar sun bayyana lamarin a matsayin abin takaici da bakin ciki, yayin da suka kuma yi kira ga gwamnatin jihar Kano da gwamnatin tarayya da su kawo dauki ga al’umma.

Bayan tattaunawa ne majalisar ta amince da kudirorin, inda ta jajanta wa al’ummar da abin ya shafa tare da addu’ar Allah ya kare afkuwar wannan lamari.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa ambaliyar ruwa ta Tiga a makon jiya ta yi barna tare da lalata gonaki da tituna da gidaje da kuma raba mazauna yankunan da muhallansu.

A halin da ake ciki, majalisar ta samu takarda daga gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje na neman amincewar nadin shugaban majalisar tare da sake nada wasu mutane biyar na kwamitin gyaran doka na jihar.

Hukumar Gyaran Shari’a ta kunshi Mai Shari’a Lawan Wada mai ritaya a matsayin shugaba, sai Sadiq Garba, Muhd, Aliyu, Yahaya Rimi, Dakta Muhammad Minjibir, Garzali Zubairu da Hauwa Yusuf a matsayin mambobi.

Wasikar dai an mika ta ne ga kwamitin shari’a na majalisar kuma an ba shi mako guda ya ba da rahoto don ci gaba da ayyukan majalisa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaDaukiGwamnatin TarayyakanoTiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalibi Dan Shekara 19 Ya Kashe Kansa A Osun

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Fasto A Filato

Related

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

8 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

1 day ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

1 day ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Next Post
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda

'Yan Bindiga Sun Sace Fasto A Filato

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.