ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambiya

by Sadiq
1 year ago
Kaciya

‘Yan majalisar dokokin kasar Gambiya, sun amince da wasu shawarwari wanda ya haramta yi wa mata kaciya, bayan da aka kada kuri’a a majalisar.

Tun a 2015 ne dai aka haramta yi wa mata kaciya a Gambiya, amma tsarin al’adar da ke da tushe ya ci gaba da yaduwa, kuma hukuncin farko da aka yanke a bara ya haifar da cece-kuce a kan dokar.

  • Tsoffin Shugabannin Sin Da Guinea Bissau Sun Taka Rawar Gani Wajen Kirkirar Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Gwamnan Zamfara Ya Samu Lambar Yabo Kan Ƙirƙiro Ayyukan Ci Gaba

Bayan zazzafar muhawara a ranar Litinin, kudirin da ke kunshe cikin rahoton kwamitin hadin gwiwa na kiwon lafiya da jinsi ya zartas da cikakken zama a majalisar, inda ‘yan majalisa 35 suka kada kuri’ar amincewa da kudurin, yayin da 17 kuma suka ki amincewa, biyu kuma ba su kada kuri’a ba.

ADVERTISEMENT

A halin yanzu an sanya ranar 24 ga watan Yuli, a mastayin ranar da za a yanke hukuncin ko za a sanya kaciyar nata a matsayin aikata laifi ko akasin haka.

Idan majalisar ta amince da hakan, Gambiya za ta zama kasa ta farko da ta janye dokar hana kaciya.

LABARAI MASU NASABA

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai

Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni

A watan Maris ne aka yi karatu na biyu inda ‘yan majalisa biyar daga cikin 53 suka kada kuri’ar kin amincewa da shi, daya kuma ya ki kada kuri’a.

Bayan karatu na biyu, kwamitin hadin gwiwa ya gudanar da taron tuntubar al’umma na kasa tare da shugabannin addini da na gargajiya, likitoci, wadanda abin ya shafa, kungiyoyin farar hula da masu kaciya da dai sauransu.

Sakamakon bincike da tuntubar da aka yi na nuni da cewa, duk nau’ikan yi wa mata kaciya cin zarafin mata ne da azabtarwa da kuma nuwawa mata wariya.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ta ce yi wa mata kaciya ba shi da wata fa’ida ga lafiya kuma yana iya haifar da zubar jini da yawa, firgita, matsalolin tunani har ma da mutuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai
Kasashen Ketare

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai

December 14, 2025
Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni
Kasashen Ketare

Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni

December 14, 2025
Rwanda Ta Musanta Hannu A Rikicin Da Ya Barke A Kibu Da DR Congo
Kasashen Ketare

Rwanda Ta Musanta Hannu A Rikicin Da Ya Barke A Kibu Da DR Congo

December 14, 2025
Next Post
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Tinubu Ya Taya Sheikh Dahiru Bauchi Murnar Cika Shekaru 100

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.