Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

An Yaba Wa Sarkin Kano Da Gwamnan Bauchi A Kan Kare Gandun Daji

by
4 years ago
in LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Sarkin Kano, Sanusi Lamido Sanusi da gwamnan jihar Bauchi, Mohammed Abdullahi Abubakar sun samu karramawa a bisa kokarinsu na bunkasa muhalli tare da kare lafiyar muhalli baki daya a fadin Nijeriya.

An karrama sune a garin Abuja jiya a yayin bude taron kungiyar masu kula da gandun daji ta kasa ‘Enbironmental Health Officers Registration Council of Nigeria (EHORECON)’.

Wadanda aka karrama matsayin Ambasada sun hada da Ministan Babban biurnin tarayya, Mallam Mohammed Musa Bello da Ministan muhalli, Mallam Ibrahim Usman Jibril da Ministan lafiya, Dakta Isaac Adewole da kuma Dakta Olugbenga Olumida sai kuma babban ragistran kungiyar, Dakta Dominic Abonyi.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Haka kuma an karrama gwamnonin Nasarawa da na Katsina, Tanko Al-makura da Alhaji Aminu Bello Masari da mukamin Ambasadan lafiyar gandun daji.

Haka kuma an karrama Sanata dakta Dalhatu Sarki Tafida da Mista Augustine Ebisille a kan gudummawarsu game da lafiyar gandun daji.

Da yakr jawabin godiya, gwamnan jihar Bauchi, Mohammed Abdullahi Abubakar ya mika godiyarsa ga kungiyar EHORECON a bisa wannan karramawar da aka yi musu, ya ce, lallai wannan karramawar za ta kara karfafa musu a kan aikin da suke yin a kare muhalli gaba daya.

Ya kuma lura da cewa, tuni jihar bauchi ta yi wa sauran birane zarra a kan matsayin da aka tsara a Abuja na water kashi 15 na kasafin kudi don bunkasa harkar lafiyar gandun daji, kamar kuma yadda kungiyar African Union ta amince.

Shi ma da ya ke karbar karramawar, gwamnan jihar Nasarawa, Tanko Al-makura ya lura da cewa, jihar Nasarawa ta shirya kara bunkasa harkokin makarantar kula da muhalli ta ‘School of Enbironmental Health.

A nasa jawabin, Ragistaran hukumar, Dakta Dominic Abonyi ya ce, hukumar ta yi wani shiri na musamman don lura da yadda hukumomi da gwamnatoci ke bayar da hankali ga harkar da ya shafi muhalli.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

FCTA Ta Kafa Kwamitin Mutum 20 Don Tsaftace Birnin Abuja

Next Post

EFCC Ta Yi Babban Kamu A Tashar Jirgin Sama Na Abuja

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
3 hours ago
0

...

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan  Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

by Sulaiman Idris
4 hours ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Kisa Kan Zargin Batanci Ga Annabi: An Tsare Wadanda Aka Kama A Gidan Gyara Hali

by
5 hours ago
0

...

An Yi Lugudan Wuta Ta Jiragen Yaki Kan Isis An Kashe Kwamandanta Bin-umar A Tabkin Chadi

Dakarun MNJTF Sun Yi Barin Wuta Kan ‘Yan Boko Haram Sun Kashe 300 A Tafkin Chadi

by Leadership Hausa
6 hours ago
0

...

Next Post
EFCC Ta Yi Babban Kamu A Tashar Jirgin Sama Na Abuja

EFCC Ta Yi Babban Kamu A Tashar Jirgin Sama Na Abuja

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: