Mahdi M Muhammad">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Ana Zargin Ta Da Satar Sarkar Gwal Na Kusan Naira 597,000

by Mahdi M Muhammad
February 1, 2021
in JAKAR MAGORI
1 min read
Ana Zargin Ta Da Satar Sarkar Gwal Na Kusan Naira 597,000
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wata mata mai shekaru 43, da aka bayyana sunan ta da Funke Benson, wacce ake zargi da satar kusan kilo 23.8 na sarkar gwal da abin hannu wanda kudinsa ya kai Naira 597,000, a ranar Laraba ta bayyana a gaban wata Kotun Majistare da ke Surulere na Jihar Legas.

‘Yan sanda sun tuhumi Benson, wacce ake zargi da laifuka biyu na hadin baki da sata.
Mai gabatar da kara na ‘yan sanda, sufeto Courage Ekhueorohan, ya fadawa kotu cewa, wacce ake kara tare da dan uwan ta da ya gudu, sun aikata laifin ne a ranar 14 ga watan Janairu, a Kasuwar Tejuosho, Yaba da ke Jihar Legas.
Ekhueorohan ya yi zargin cewa, wacce ake karar, wacce ke tare da wani mutum, ta shiga shagon Abubakar Ali, don sayen sarkar gwal, a inda ba zako ba tsammani, suka lacce shi
Mai gabatar da kara ya gabatar da cewa, yayin da wacce ake kara da abokin aikin na ta ke cinikin sarkar gwal, sai mutumin (shi abokin aikin na ta) ya nemi fita don yi fitsari, dawowar da bai yi ba kenna shagon Ali.
Ya ce, lokacin da Ali (mai shigar da kara) ya lura da sarkar gwal da abin hannu sun bata, sai ya tambayi wacce ake kara, a inda ta musanta cewa ba ta dauka ba. An tsare wacce ake kara a shagon, yayin da Ali ya kira ‘yan sanda.
Laifin, in ji shi, ya ci karo da sashi na 287 da 411 na dokar aikata manyan laifuka ta jihar Legas, ta shekarar 2015.
Benson, ta musanta aikata laifin.
Alkalin kotun M.I. Dan-Oni ya bayar da belin wacce ake kara a kan kudi Naira 200, 000 tare da mutane biyu wadanda za su tsaya ma ta.
Alkalin ta dage sauraron karar har sai ranar 3 ga watan Fabrairu, domin ci gaba da shari’a.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Magidanci Ya Yi Tattakin Kilomita 420 Bayan Samun Sabani Da Matarsa

Next Post

Za A Samu Kamar Ronaldo Nan Gaba Kadan – Roberto Carlos

RelatedPosts

Guba

Hassada Ya Sa Matata Sanya Wa Dan Kishiyarta Guba – Miji

by Mahdi M Muhammad
15 hours ago
0

Abdulwasiu Musa, mijin wata mata da ta sanya wa danta...

Ya Farka Mintoci Kafin Jana’izarsa

by Mahdi M Muhammad
15 hours ago
0

Wani matashi mai suna Kumar Marewad, dan shekara 17 daga...

An Cire Rayayyen Kyankyaso Daga Kwanyar Wata Mata

by Mahdi M Muhammad
16 hours ago
0

Wata mata mai suna Selbi 'yar shekaru 42 daga Chennai,...

Next Post
Ronaldo

Za A Samu Kamar Ronaldo Nan Gaba Kadan – Roberto Carlos

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version