ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
APC

Kamar yadda aka shaida a 2013, lokacin da hadakar jam’iyyun siyasa da fusatattun mambobin na jam’iyya mai mulki ta PDP, lokacin da suka hadu suka kafa jam’iyyar APC tare da kayar da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da jam’iyyarsa a zaben 2015.

Saboda haka, gabanin zaben 2027, irin wannan al’amarin yana faru tare da ‘yan siyasa da aka fusata da kuma wadanda ke jin haushi a cikin APC, da shugabannin jam’iyyar adawa sun mika takardunsu ga hukumar zaben mai zaman kanta kasa (INEC) don kafa hadakan jam’iyya ta ADA don hambarar da APC.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Shugaban kasa, Bola Tinubu, wanda shi ma yana daga cikin mamba a cikin hadakar a 2013, wanda daga bisani aka samar da APC, kuma har ya kawo karshen mulkin PDP, shin ko shugabannin adawa sun shirya amfani da irin wannan dabarar don kwace mulki a 2027?.

ADVERTISEMENT

Bisa yadda aka fara gwagwarmayan zaben 2027 a cikin hanzari, Tinubu bai da lokacin batawa wajen fitar da lissafin siyasarsa lokacin da aka samu labarin murabus din shugaban jam’iyyar APC, Dakta Abdullahi Ganduje a ranar Jumma’a. Murabus dinsa na bazata ya haifar da rudani da saka alaman tambaya ga sakateriyar jam’iyyar ta kasa.

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya mika takardar ajiye aiki ga kwamitin zartarwa na jam’iyyar a ranar Juma’a, yana mai bayyana dalilansa na rashin lafiya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

Tun daga lokacin da ya yi murabus, ana ta bayar da dalilai da dama kan aje mukaminsa na bazata. Yayin da wasu ke cewa lamarin zanga-zangar da aka yi a taron masu ruwa da tsaki na APC a yankin Arewa maso Gabas da aka gudanar a Jihar Gombe game da rashin jaddada sunan mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima na goyon bayan tazarcen Tinubu a 2027, wasu kuwa sun ce zargin cin hanci da rashawa ake masa shi ne abin da ya kawo karshen mukaminsa.

Yayin da wasu suka yi tunanin cewa duk da zanga-zangar da mambobin jam’iyyar suka yi a sakateriyar jam’iyyar na kasa, an zargi Ganduje da yin amfani da masu sauya sheka da ke shiga jam’iyyar wajen sauya tsarin jam’iyyar.

Wasu na ganin mai yiwuwa saboda dawowar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabiu Kwankwaso ya taka muhimmiyar rawa wajen yanke shawarar shugaban na fitar da Ganduje ta hanyar yin murabus.

Masu sharhi kan al’amurar siyasa na ganin cewa idan har dai Ganduje na matsayin shugaban APC, zai yi matukar wuya Kwankwaso ya koma cikin jam’iyyar, saboda yadda ake takun saka tsakanin Ganduje da Kwankwaso, sannan kuma Tinubu ya dade yana zawarcin Kwankwaso wajen shigowa APC. Sun kara da cewa kan wannan tunanin ne aka yi zaton cewa barin Ganduje wani yunkuri ne na musamman don saukaka hanyan komawar Kwankwaso zuwa APC, wanda zai iya rage adawa a arewa da kuma karfafa Tinubu a 2027.

A cewarsu, a fili yake, daga cikin manyan matakin siyasar da Tinubu ya dauka domin sharar fage na tunkarar zaben 2027 shi ne, saita hanyar da za ta bulle masa zuwa 2027. Misali, a ranar Alhamis da ta gabata, shugaban ya tabbatar da sulhu tsakanin Gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara da Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, duk suna nuni da wani lissafin Tinubu na kara karfi a dukkan bangarorin Nijeriya.

Tare da ficewar Ganduje, masu ruwa da tsaki na jam’iyyar daga yankin arewa ta tsakiya ba su bata lokaci ba wajen sabunta kiransu na samun kujerar shugabancin jam’iyyar na kasa.

Tun lokacin da aka kafa APC a 2013, APC ta yi shugabanni guda shida da suka hada da Cif Bisi Akande (2013 zuwa 2014), Cif John Odigie-Oyegun (2014 zuwa 2018), Kwamared Adams Oshiomhole (2018 zuwa 2020), Mai Mala Buni (2020 zuwa 2022), Sanata Abdullahi Adamu (2022 zuwa 2023) da kuma Dakta Abdullahi Umar Ganduje (2023 zuwa 2025).

Matakin Tinubu na sadaukar da Ganduje don dakile barazanar shugabannin adawa kafin zaben 2027 zai kara shaida ga wadanda suke da shakka cewa Tinubu har yanzu yana da kwarewa a cikin harkokin. Lokaci ne kadai zai tabbatar da babuwan da zai faru a 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.