• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka shaida a 2013, lokacin da hadakar jam’iyyun siyasa da fusatattun mambobin na jam’iyya mai mulki ta PDP, lokacin da suka hadu suka kafa jam’iyyar APC tare da kayar da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da jam’iyyarsa a zaben 2015.

Saboda haka, gabanin zaben 2027, irin wannan al’amarin yana faru tare da ‘yan siyasa da aka fusata da kuma wadanda ke jin haushi a cikin APC, da shugabannin jam’iyyar adawa sun mika takardunsu ga hukumar zaben mai zaman kanta kasa (INEC) don kafa hadakan jam’iyya ta ADA don hambarar da APC.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Shugaban kasa, Bola Tinubu, wanda shi ma yana daga cikin mamba a cikin hadakar a 2013, wanda daga bisani aka samar da APC, kuma har ya kawo karshen mulkin PDP, shin ko shugabannin adawa sun shirya amfani da irin wannan dabarar don kwace mulki a 2027?.

Bisa yadda aka fara gwagwarmayan zaben 2027 a cikin hanzari, Tinubu bai da lokacin batawa wajen fitar da lissafin siyasarsa lokacin da aka samu labarin murabus din shugaban jam’iyyar APC, Dakta Abdullahi Ganduje a ranar Jumma’a. Murabus dinsa na bazata ya haifar da rudani da saka alaman tambaya ga sakateriyar jam’iyyar ta kasa.

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya mika takardar ajiye aiki ga kwamitin zartarwa na jam’iyyar a ranar Juma’a, yana mai bayyana dalilansa na rashin lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Tun daga lokacin da ya yi murabus, ana ta bayar da dalilai da dama kan aje mukaminsa na bazata. Yayin da wasu ke cewa lamarin zanga-zangar da aka yi a taron masu ruwa da tsaki na APC a yankin Arewa maso Gabas da aka gudanar a Jihar Gombe game da rashin jaddada sunan mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima na goyon bayan tazarcen Tinubu a 2027, wasu kuwa sun ce zargin cin hanci da rashawa ake masa shi ne abin da ya kawo karshen mukaminsa.

Yayin da wasu suka yi tunanin cewa duk da zanga-zangar da mambobin jam’iyyar suka yi a sakateriyar jam’iyyar na kasa, an zargi Ganduje da yin amfani da masu sauya sheka da ke shiga jam’iyyar wajen sauya tsarin jam’iyyar.

Wasu na ganin mai yiwuwa saboda dawowar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabiu Kwankwaso ya taka muhimmiyar rawa wajen yanke shawarar shugaban na fitar da Ganduje ta hanyar yin murabus.

Masu sharhi kan al’amurar siyasa na ganin cewa idan har dai Ganduje na matsayin shugaban APC, zai yi matukar wuya Kwankwaso ya koma cikin jam’iyyar, saboda yadda ake takun saka tsakanin Ganduje da Kwankwaso, sannan kuma Tinubu ya dade yana zawarcin Kwankwaso wajen shigowa APC. Sun kara da cewa kan wannan tunanin ne aka yi zaton cewa barin Ganduje wani yunkuri ne na musamman don saukaka hanyan komawar Kwankwaso zuwa APC, wanda zai iya rage adawa a arewa da kuma karfafa Tinubu a 2027.

A cewarsu, a fili yake, daga cikin manyan matakin siyasar da Tinubu ya dauka domin sharar fage na tunkarar zaben 2027 shi ne, saita hanyar da za ta bulle masa zuwa 2027. Misali, a ranar Alhamis da ta gabata, shugaban ya tabbatar da sulhu tsakanin Gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara da Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, duk suna nuni da wani lissafin Tinubu na kara karfi a dukkan bangarorin Nijeriya.

Tare da ficewar Ganduje, masu ruwa da tsaki na jam’iyyar daga yankin arewa ta tsakiya ba su bata lokaci ba wajen sabunta kiransu na samun kujerar shugabancin jam’iyyar na kasa.

Tun lokacin da aka kafa APC a 2013, APC ta yi shugabanni guda shida da suka hada da Cif Bisi Akande (2013 zuwa 2014), Cif John Odigie-Oyegun (2014 zuwa 2018), Kwamared Adams Oshiomhole (2018 zuwa 2020), Mai Mala Buni (2020 zuwa 2022), Sanata Abdullahi Adamu (2022 zuwa 2023) da kuma Dakta Abdullahi Umar Ganduje (2023 zuwa 2025).

Matakin Tinubu na sadaukar da Ganduje don dakile barazanar shugabannin adawa kafin zaben 2027 zai kara shaida ga wadanda suke da shakka cewa Tinubu har yanzu yana da kwarewa a cikin harkokin. Lokaci ne kadai zai tabbatar da babuwan da zai faru a 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ganduje
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Next Post

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 day ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 days ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

1 week ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

1 week ago
Next Post
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

LABARAI MASU NASABA

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.