• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Dakatar Da Kara Kudin Wutar Lantarki A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Dakatar Da Kara Kudin Wutar Lantarki A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hankoron Nijeriya na shiga sahun kasashe masu bunkasar tattalin arzki da masana’antu ya rushe a ‘yan shekarun nan ne saboda rashin tsayayyar wutar lantarki a sassan kasa.

Ga kasar da ke da al’umma fiye da mutum miliyan 200 a yanzu ana iya samar da karfin wutan lantarki ne da ya kai megawatt 13,000 kacal, amma kuma megawatt 4,000 ne kawai ake iya rarraba wa al’umma saboda matsalolin da suka shafi rashin ingantattun na’u’rorin rarraba wutar lantarkin. Ba abin mamaki ba ne yadda ake samun yawaitar rashin wuta da lalacewar na’urorin rarraba wutar, abin da kuma yake haifar da koma baya ga zamantakewa da harkokin kasuwanci a sassan Nijeriya.

  • Amsar Xi Jinping Ta Ba Duniya Damar Fahimtar Tsarin Binciken Hada-hadar Kudin Na Kasar Sin
  • Gwamnan Zamfara Ya Rage Yawan Adadin Ma’aikatun Jihar Daga 28 Zuwa 16

Watakila saboda ganin muhimmancin wutar lantarki ga harkokin raya kasa ya sanya Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu a kan dokar gyara da kwaskwarima ga bangaren wutar lantarkin Nijeriya a cikin kwanaki 10 da hawansa karagar mulkin, ya sanya hannu a kan dokar wutar lantarki ta shekara 2023 inda aka maye gurbinta da dokar ta shekara 2005, inda aka sake fasalin dokar don ta yi daidai da wannan zamanin da ake ciki.

Dokar za ta samar da yanayin da zai karfafa masu zuba jari a bangaren wutar lantarki musamman a kan abin da ya shafi rarraba wutar lantarki, ta yadda kamfanoni masu zaman kansu za su shigo don aiwatar da tadane-tanaden dokar don amfanin al’ummar kasa da bunkasar tattalin arziki Nijeriya.

A cikin sabuwar dokar, an sahallewa jihohi su bayar da lasisi ga masu zuba jari don su samar da kananan tashoshin samar da wutar lantarki a cikin jihohinsu amma dokar ta haramta rarraba wuta a tsakanin jihohi, ba kamar yadda abin yake a can baya ba.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

A karkashin sabuwar dokar ta shekarar 2023, Hukumar Rarraba Wutar Lantarki (NERC) za ta samu damar sanya ido a kan harkokin rarraba wutar lantarki a Nijeriya ba tare da ta yi katsalandan da dokar da da ta ba jihohi ikon gudanar da nasu harkokin ba, amma kuma doka ta bata hurumin sa ido a kan yadda al’amurra ke tafiya a jihohin gaba daya.

Dokar ta kuma bayyana yadda hukumar NERC za ta mika harkokin gudanarwa ga kamfanonin da aka kafa na wutar lantarki a jihohi ba tare da an samu wata matsala ba. Amma kuma NERC za ta ci gaba da sanya ido a kan yadda wadannan kamfanonin ke gudanar da aikinsu har sai jihohin sun kafa nasu dokokin da za su sa ido a kan harkokin kamfanonin da aka kafa. A halin yanzu jihohin Legas, Edo, da Kaduna ne kawai suka samar da dokokin sa ido a harkokin kasuwancin wutar lantarki a Nijeriya.

Wani sabon lamari a cikin sabuwar dokar ya hada da amincewar da aka yi mutum na iya samar wa kansa wutar lantarki don amfanin kansa amma wutar da bai wuce megawatt 1 (MW) ba, amma kuma hukumar NERC ke a ikon sanya ido a kan irin wannan shirin tare da sabunta da lasisi daga lokaci zuwa lokaci.

A mastayinmu na gidan jarida, muna masu yaba wa shugaban kasa a kan yadda ya sa hannu a kan sabuwar dokar, musamman ganin yadda masu ruwa da tsaki suka dade suna ta kiran a samar da yanayin da bangaren wutar lantarki zai yi bunkasar da ta dace, dokar ta fitar da dukkan matsalolin da ke haifar da cikas a kokarin bunkasar bangaren samar da wutar lantarki a Nijeriya, dokar kuma za ta karfafa tare da jawo masu zuba jari a ciki da wajen kasar nan wanda ba sai an fada ba hakan zai samar da bunkasar tattalin arziki saboda manya da kananan masa’nantun Nijeriya za su bunkasa, abin kuma da zai taimaka wajen samar da aikin yi ga dimbin matasan Nijeriya.

Karin jihohi da kanfanoni masu zaman kansu a bangaren samar da wutar lantarki zai karfafa bangaren wutar lantarki ta hanyar samar da sabbin kayan aiki da kwararru daga kasashen waje wadanda za su bayar da gudummawarsu da sabuwar fasahar samar da rarraba wuta lantarkin.

In har aka samu karin jihohi da sabbin kamfanoni a bangaren kamar an yi maganin abin da ya shafi yadda ake samun matsala wajen karbar kudaden wuta ne daga hannun al’umma, hakan zai kai ga samun karin kudaden shiga ga jihohi wanda zai kuma kai ga aiwatar da ayyukan raya kasa da karin zuba jari.

Sau da dama a Nijeriya babbar matsalar da aka fi fuskanta ita ce na aiwatar da tsare-tsare da wai kafa doka ba, a kan haka muke kira da a tabbatar an aiwatar da dokar yadda ya kamata.

Karin kudin wuta da aka yi a kwanan nan da kashi 40 abu ne da ya tayar da hankulan al’ummar Nijeriya, wannan na zuwa ne a yayin da ake fuskantar hauhawar farashin kayan masarufi, tabbas ya kamata a duba wannan karin da aka yi da nufin samar da yanayin da za a rage wa al’umma matsalolin da suke ciki.

Tuni kungiyar kwadago ta NLC ta nemi a gaggauta dakatar da karin kudin wutar lantarkin sai zuwa wani lokaci da al’murra suka daidaita, wannan na da matukar muhimmanci kuma ya kamata gwamnati ta sanya baki don ganin a samar da daidaito a kudin da za a kara don tabbas al’umma da fama matsalar rayuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kara KudiWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Rage Yawan Adadin Ma’aikatun Jihar Daga 28 Zuwa 16

Next Post

Tirka-tirkar Daliba Ejikeme Mmesoma: Masani Ya Tona Asirin Yadda Ake Sauya Sakamakon JAMB Na Bogi

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

4 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

6 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

8 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

10 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku MiÆ™a Wuya – Ribadu Ya GargaÉ—i ‘Yan Bindiga

13 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

23 hours ago
Next Post
Tirka-tirkar Daliba Ejikeme Mmesoma: Masani Ya Tona Asirin Yadda Ake Sauya Sakamakon JAMB Na Bogi

Tirka-tirkar Daliba Ejikeme Mmesoma: Masani Ya Tona Asirin Yadda Ake Sauya Sakamakon JAMB Na Bogi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

July 30, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

July 30, 2025
Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

July 30, 2025
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

July 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

July 30, 2025
’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.