• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Gwamnati Ta Muhimmanta Jin Dadin ‘Yan Nijeriya

by Sulaiman
3 years ago
Nijeriya

Ga yawancin ‘yan Nijeriya wannan ba lokaci ne na walwala a harkokin yau da kullum ba, don kuwa kusan dukkan harkokin yau da kullum na al’umma sai tashi yake yi a kullum garin Allah ya waye lamarin yana kokarin kaiwa matakin bantsoro.

Kuma babu wani fatan za a warware matsalar a nan kusa, babban abin da ke a gaban mahukunta a halin yanzu shi ne na yadda za su cigaba da rike madafun ikon tafiyar da kasa a zaben shekarar 2023, a kan haka mutum zai iya cewa, babu wani nau’i na alamun tafiyar da mulki a kasar nan a gaban su gaba daya.

  • Harin Kuje Da Tawagar Buhari: Ya Kamata A Sauya Shugabannin Tsaro – Alhaji Ibrahim

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, a halin yanzu yakamata dukkan matakan gwamnati su dawo da akalar su a kan harkokin da suka shafi a’umma don kuwa wannan shi ne nauyi na farko da suka daukar wa kansu kuma shi ne yafi muhimmanci a kan dukkan alkawurran da suka yi a yayin da suke yakin neman zabe da kuma rantsuwar kama aiki da suka yi tun da farko.

Muna jawo hankalin masu tafiyar da gwamnati a dukkan matakai na rashin dacewar yadda aka mayar da al’umma baya, sun zama wasu da basu da wata fata na cimma wani muhimmin abu a raywarsu.

Yana da matukar sauki ‘yan Nijeriya su fahimci cewa, matsalolin da ake fuskanta a sassan kasar musamman abin da ya shafi tafiyar da rayuwa suna kara karuwa ne a kullum kuma babu wata rana da ake tunanin kawo karshen su.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Tun daga darajar Naira zuwa yadda wutar lantarki ta tabarbare da kuma yadda ake samun hauhawar farashin kayyakikn abnici, abin takaicin kuma shi ne ko a jikin ‘yan siyasar mu, duk kuwa da muna cikin kakar zabe inda yakamata a rinka tattauna irin wadannan matsaloli tare da bayanin yadda za su magance su. Ba abin da ya shafe su don kuwa a wannan zamanin sayen kuri’a ake yi ba maganar abin da aka kuduri yi wa al’umma ba.

Wannan jaridar ta lura da cewa, lallai kafin a gudanar da tarukan siyasa tare da zabar ‘yan takara a manyan jam’iyyunmu darajar Naira ta fadi warwars amma lamarin ya kara tabarbarewa ne a lokacin da aka shiga harkokin siyasar gadangadan saboda yadda aka rika kasha wa wakilai masu zabe (Deliget) kudadden kasashe wajen don sayen kuri’arsu.

‘Yan Nijeriya na kallo Naira ya ta faduwa irin faduwar da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan, wanda hakan kuma ya shafi harkokin saye sayarwa a cikkin al’umma.

A ra’ayinmu babu wata bangare na tattalin arzikin kasar nan daya fi fuskantar matsalar kamar bangaren wutar lantarki.

A tsawon watanni ke nan farashin iskar gas, dizel da man fetur suka yi tashin gwauron zabi, layuka sun kara bayyana a gidajen mai kuma babu wanda zai fada maka ranar da ake ganin za a kawo karshen lamarin.

Lamarin ya kara tabarbarewa ne ta yadda aka samu labarin matsalar da ta fadawa bangaren samar da wutar lantarki inda (National grid) ya rushe.

Wadanna matsalolin sun kuma kara tayar da hankali ne ganin yadda farashin kayyakin abinci suka cigaba da ta’azzara kusan suna neman fin karfin masu karamin karfi, a halihn yanzu koda fiya wata yana neman zama wata alfarma ga ‘yan Nijeriya.

Matsalar tsaron da ake fuskanta a sasan kasar nan ya kara canza tsananin rikicin da ake fuskanta, mun yi magana sau da dama a kan wannan bangaren kuma bai kamata mu sake makalewa wajen tattauna wannan ba.

Wasu na bayar da uzurin cewa, gwamnatin nan na bayar da muhimmanci ga samar da hanyoyi da wasu aikace-aikace na raya kasa, amma a nan muna masu cewa, tabbass rayuwar al’umma yafi wani gyaran titi da za a yi, ina amfanin badi ba rai?, yakamata a bayar da karfi wajen bunkasa rayuwar al’umma.

A yanayin da manyan makarantunmu ke kulle, asibitoci suka zama kufai, kashe-kashe ya zama ruwan dare, sai a fara tunanin ko gwamnnti bata san abin daya kamata ta muhimmantar ba kenan.

Muna kira ga gwamnati a dukkan matakai su dauki abubuwan da suka shafi rayuwar al’umma da muhimmanci, Allah ya taimake mu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.