• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Gwamnati Ta Muhimmanta Jin Dadin ‘Yan Nijeriya

by Sulaiman
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga yawancin ‘yan Nijeriya wannan ba lokaci ne na walwala a harkokin yau da kullum ba, don kuwa kusan dukkan harkokin yau da kullum na al’umma sai tashi yake yi a kullum garin Allah ya waye lamarin yana kokarin kaiwa matakin bantsoro.

Kuma babu wani fatan za a warware matsalar a nan kusa, babban abin da ke a gaban mahukunta a halin yanzu shi ne na yadda za su cigaba da rike madafun ikon tafiyar da kasa a zaben shekarar 2023, a kan haka mutum zai iya cewa, babu wani nau’i na alamun tafiyar da mulki a kasar nan a gaban su gaba daya.

  • Harin Kuje Da Tawagar Buhari: Ya Kamata A Sauya Shugabannin Tsaro – Alhaji Ibrahim

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, a halin yanzu yakamata dukkan matakan gwamnati su dawo da akalar su a kan harkokin da suka shafi a’umma don kuwa wannan shi ne nauyi na farko da suka daukar wa kansu kuma shi ne yafi muhimmanci a kan dukkan alkawurran da suka yi a yayin da suke yakin neman zabe da kuma rantsuwar kama aiki da suka yi tun da farko.

Muna jawo hankalin masu tafiyar da gwamnati a dukkan matakai na rashin dacewar yadda aka mayar da al’umma baya, sun zama wasu da basu da wata fata na cimma wani muhimmin abu a raywarsu.

Yana da matukar sauki ‘yan Nijeriya su fahimci cewa, matsalolin da ake fuskanta a sassan kasar musamman abin da ya shafi tafiyar da rayuwa suna kara karuwa ne a kullum kuma babu wata rana da ake tunanin kawo karshen su.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

Tun daga darajar Naira zuwa yadda wutar lantarki ta tabarbare da kuma yadda ake samun hauhawar farashin kayyakikn abnici, abin takaicin kuma shi ne ko a jikin ‘yan siyasar mu, duk kuwa da muna cikin kakar zabe inda yakamata a rinka tattauna irin wadannan matsaloli tare da bayanin yadda za su magance su. Ba abin da ya shafe su don kuwa a wannan zamanin sayen kuri’a ake yi ba maganar abin da aka kuduri yi wa al’umma ba.

Wannan jaridar ta lura da cewa, lallai kafin a gudanar da tarukan siyasa tare da zabar ‘yan takara a manyan jam’iyyunmu darajar Naira ta fadi warwars amma lamarin ya kara tabarbarewa ne a lokacin da aka shiga harkokin siyasar gadangadan saboda yadda aka rika kasha wa wakilai masu zabe (Deliget) kudadden kasashe wajen don sayen kuri’arsu.

‘Yan Nijeriya na kallo Naira ya ta faduwa irin faduwar da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan, wanda hakan kuma ya shafi harkokin saye sayarwa a cikkin al’umma.

A ra’ayinmu babu wata bangare na tattalin arzikin kasar nan daya fi fuskantar matsalar kamar bangaren wutar lantarki.

A tsawon watanni ke nan farashin iskar gas, dizel da man fetur suka yi tashin gwauron zabi, layuka sun kara bayyana a gidajen mai kuma babu wanda zai fada maka ranar da ake ganin za a kawo karshen lamarin.

Lamarin ya kara tabarbarewa ne ta yadda aka samu labarin matsalar da ta fadawa bangaren samar da wutar lantarki inda (National grid) ya rushe.

Wadanna matsalolin sun kuma kara tayar da hankali ne ganin yadda farashin kayyakin abinci suka cigaba da ta’azzara kusan suna neman fin karfin masu karamin karfi, a halihn yanzu koda fiya wata yana neman zama wata alfarma ga ‘yan Nijeriya.

Matsalar tsaron da ake fuskanta a sasan kasar nan ya kara canza tsananin rikicin da ake fuskanta, mun yi magana sau da dama a kan wannan bangaren kuma bai kamata mu sake makalewa wajen tattauna wannan ba.

Wasu na bayar da uzurin cewa, gwamnatin nan na bayar da muhimmanci ga samar da hanyoyi da wasu aikace-aikace na raya kasa, amma a nan muna masu cewa, tabbass rayuwar al’umma yafi wani gyaran titi da za a yi, ina amfanin badi ba rai?, yakamata a bayar da karfi wajen bunkasa rayuwar al’umma.

A yanayin da manyan makarantunmu ke kulle, asibitoci suka zama kufai, kashe-kashe ya zama ruwan dare, sai a fara tunanin ko gwamnnti bata san abin daya kamata ta muhimmantar ba kenan.

Muna kira ga gwamnati a dukkan matakai su dauki abubuwan da suka shafi rayuwar al’umma da muhimmanci, Allah ya taimake mu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Next Post

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

Related

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

4 days ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

5 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

5 days ago
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

2 weeks ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

3 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

3 weeks ago
Next Post
Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

September 3, 2025
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

September 3, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

September 3, 2025
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

September 3, 2025
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

September 3, 2025
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

September 3, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

September 3, 2025
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

September 3, 2025
Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

September 3, 2025
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.