• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 month ago
in Ra'ayinmu
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne, Muyiwa Ige, da ga marigayi Cif Bola Ige, ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu, da sake bijiro da batun kisan da aka yi wa mahaifinsa, musamman domin a bankado da wadanda suka aikata kisan, tare da hukunta su.

Yau dai, shekaru 24 ke nan, da aka halka Ige, a gidansa da ke a garin Ibadan, a jihar Oyo, wanda aka kashe shi, a ranar 23 na watan Disambar 2001.

  • Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma
  • Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

A cikin rokon da Muyiwa ya yiwa Tinubu na sake bijro da batun kisan na mahaifinsa, ya bayyana irin halin gallazawa da mahaifinsa, ya tsinci kansa a lokacin kisan, musamman duba da cewa, mahaifin na sa, akawai wasu muradu, na rayuwarsa, da ya so ya cimma, amma kisan ya kawo karashen hakan.

An dai hallaka Ige ne, a lokacin da yake rike da mukamin Minitan Shari’a kuma Atoni Janar na kasa.

Bayan gaza cafko wadanda ake zargi da aikata kaisan da kuma yadda akai ta kai Gwaro da Mari a gaban kotu kan batun a wadancan shekaru, haka dai lamarin ya sha ruwa.

Labarai Masu Nasaba

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

Koda ya ke dai, a lokacin ‘yansanda sun yi nisa ban gudanar bincike, amma babu wanda suka iya kamawa, kuma ba a kara shigar da wata sabuwar kara a gaban kotu ba, duk tsawon wadannan shekarun.

Wannan bukatar da Muyiwa ya biro da ita, tamkar bude wani sabon babi ne, kan batun hallaka manyan mutane a kasar, wadda za a iya cewa, tun daga 1999, har zuwa yau, amma shiru ake ji, kan daukar wani kwakwaran mataki.

A wani taro a kwanan baya, babban Lauya SAN Cif Kanu Agabi, ya bijiro da zargin yadda ake gaza hukunta masu aikata manyan laifuka a kasar, inda kuma ake samun dogon jan kafa, kan shari’ar da ta shafi, marasa karfi a kasar.

Wannan zargin na Kanu, ya nuna a zahiri, yadda aka yiwa bangaren shari’ar kasar, rikon Sakainar Kashi, musamman wajen gaza cafko, masu aikata manyan laifuka, domin su fuskanci hunci.

Bugu da kari, a kasidar da ya gabatar a a taron jamia’r NOUN, tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa, yin gaskiya wanzar da zaman lafiya tabbatar da tsaro, tare da bai wa ko wanne dan kasa hakkinsa, su ne, ginshikin da ke bunkasa tattalin arzikin kasa.

Sai abin dubi a nan, wannan yawabin na, Cif Olusegun, ya kasance yana cin karo da juna, domin a lokacin yana kan Karagar shugabancin kasar ne, aka kashe marigayi Ige.

Cafko irin wadannan masu halka manyan mutane a kasar domin a hukunta su, kamar yadda dokar kasa ta tanada, ba wai kawai hakan zai samar da salama ga ahalinsu bane, musamman duba da yadda suka yi babban rashi, amma hakan zai kuma zama wani babban abin ci gaba, ga kasar.

Kazalka, kamo su din, zai zama tamkar wani gargadi ne, da zai nuna cewa, akwai hukuncin da kasar ta tanadar, ga masu aikata irin wannan halin na rashin imani.

A nan, wannan Jaridar, ta yi waiwaye kan kisan rashin imani da aka akatawa mataimakin shugaban PDP na shiyyar Kudu Maso Kudu Cif Aminasoari Kala (A.K) Dikibo shekaru 21 da suka gabata.

Abin takaici, an hallaka shi ne, da tsayiyar rana a kan wata babbar hanya, a ranar ga 4 Fabiraurun 2004.

Sai dai, har zuwa yanzu, babu wani kokari da rundunar ‘yansanda ko hukumar DSS suka yi, na bankado makasan.

Kazalika, tshohon mataimakin shugaba na Kudu Maso Kudu, rusasshiyar jami’iyyar ANPP Marshal Sokari Harry, an kashe shi a Abuja a ranar 5 ga watan Maris na 2003 a lokacin zaben shugaban kasa

Hakazalika, an yiwa dan siyasa Anthony Olufunsho Williams, kisan gilla a gidansa da ke a rukunin gidaje na Dolphin, a jihar da ke Ikoyi, Legas, a ranar 27 ga watan Julin 2005.

An hallaka shi ne, yayin da ake shirin tsayar da shi, dan takarar gwamna a PDP na jihar Legas.

Rashin daukar matakin, na kara zubur da kimar Nijeriya a idon duniya.

Hakazalika, hakan ya sanya, wasu hukumomin a jihohin kasar nan, ke shawartar alumomin, da su dauki matakan kare kansu, daga hare-haren da aka kai wa jama’a, wanda hakan karara, ya nuna gazawar gwamnatin kasar, na kare rayuka da kuma dukiyoyin ‘yan kasar.

A saboda haka, akwai bukatar, a yiwa bangaren shari’a na kasar garanbawul, domin a lalubo da mafita kan lamarin.

Ko da yake dai, majalisar kasa na kan yunkurin sabunta dokar zabe ta 2022.

A matsayin mu a wannan Jaridar, mun kasance kan gaba wajen yin kira da a samar da sauye-sauye a bangaren shari’a, musamman domin a dawo da kimar da bangaren yake da shi, kamar yadda aka san shi, a shekarun baya.

A tunanin mu, samar da wannan sauye-sauyen a bangaren shari’ar, za a samar da kyakyawan yanayi a bangaren na shari’a, tare da gaggawar daukar makai, kan irin wannan kisan gillar da ake yiwa manyan kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Next Post

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

7 days ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

2 months ago
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Ra'ayinmu

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

3 months ago
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
Ra'ayinmu

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

3 months ago
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara
Ra'ayinmu

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

3 months ago
Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

4 months ago
Next Post
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.