• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canjin Kudi: Dole Ne Mu Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa —Matawalle

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Canjin Kudi: Dole Ne Mu Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa —Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Bello Matawalle na Jihar Zamfara, ya ce shi da takwarorinsa sun kai Gwamnatin Tarayya gaban kotun koli ne domin ceto tattalin arzikin kasar nan daga durkushewa.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya bayar da rahoton cewa, gwamnoni uku na jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara sun maka gwamnatin tarayya a kotun koli, inda suke neman ta dakatar da shirin sauya fasalin Naira na Babban Bankin Nijeriya (CBN).

  • Mata Na Da Rawar Da Za Su Taka Wajen Ci Gaban Al’umma Idan Aka Ba Su Dama – Maryam Abacha
  • Da ɗumi-ɗuminsa: Mataimakin Gwamnan Sakkwato Ya Koma APC

NAN ya kuma ruwaito cewa a ranar Laraba ne kotun koli ta dakatar da CBN daga aiwatar da wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu na daina amfani tsofaffin takardun kudi.

Wata sanarwa da aka fitar a Gusau a ranar Alhamis, ta hannun mai ba shi shawara ta musamman kan wayar da kan jama’a da yada labarai da sadarwa, Malam Zailani Bappa, ta ce wadanda suka yi adawa da matakin da suka dauka da nasarar da suka samu a kotun koli sun yi kuskure.

“Bayan kalaman rashin gaskiya da ke biyo bayan hukuncin da Kotun Koli ta kasa ta yanke na saurare da kuma aiwatar da bukatar gwamnonin da suka yi nasara a kan musayar Naira, Matawalle ya bayyana ra’ayinsu a matsayin siyasa kawai.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

“Na tabbata cewa wadanda suka yi adawa da matakin da muka dauka na Kotun Koli ko dai sun rude ne ko kuma sun makantar da su saboda son zuciya.

“Ni da takwarorina na jihohin Kaduna da Kogi mun ga ya dace mu tunkari kotun koli domin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga fadawa cikin mawuyacin hali.

“Kuma don kawar da radadin da talakawan Nijeriya ke fama da shi ta fuskar karancin kudi na tsofaffi da sabbin kudin Naira,” in ji Matawalle.

A cewarsa, yana da kyau a ce dole ne CBN da bankunan kasuwanci su samar da sabbin takardun Naira domin gudanar da harkokin kasuwanci na yau da kullum kafin a ayyana daina amfani da tsofaffin takardun kudi.

Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa da kalaman abokan hamayyarsa na siyasa, inda ya kara da cewa jam’iyyun siyasar da ke kalubalantar hukuncin kotun ba su da muradin kasar nan a zuciya.

“Hukuncin da alkalan kotun koli masu hikima da mutuntawa suka yanke kan wannan lamari, ita ce hanya mafi dacewa don magance matsalar da ake fama da ita da kuma sakamakon da ke tafe a halin yanzu.”

Matawalle ya kara da cewa, “A wannan mawuyacin lokaci na mika mulki, kishin kasa ne kawai ke gabanmu, mu ajiye tunanin siyasa a gefe tare da magance kalubalen da ke gabanmu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariCanjin KudiCBNHukunciKadunaKogiKotun KoliMatawalleNairaWa'adiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

Next Post

Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

Related

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

3 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

7 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

10 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

21 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

1 day ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

1 day ago
Next Post
Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.