ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Na Da Rawar Da Za Su Taka Wajen Ci Gaban Al’umma Idan Aka Ba Su Dama – Maryam Abacha

by Bello Hamza
3 years ago
Abacha

Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Marigayi Janar Sani Abacha, wato Hajiya (Dr) Maryam Abacha ta ja hankalin al’umma musamman mazaje da su rika bai wa mata dukkanin wata dama da ‘yanci na neman ilimi da aiki ko sana’a domin ci gaban al’umma baki daya.

 

Dr Maryam Abacha ta bayyana hakan ne a ranar Talata a yayin da take ganawa da manema labarai a gidanta dake birnin Tarayya Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

Hajiya Maryam ta ce mata suna da tasirin gaske wajen gina ingantacciyar al’umma, domin su ke tarbiyyar al’umma, inda ta yi amfani da wannan dama wajen kira na musamman ga mazaje da su rika bai wa matansu dama ta neman ilimi da aiki ko sana’a.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Dr Maryam ta ce maza musamman a arewacin Nijeriya ba su cika taimakawa matansu wajen cimma burinsu ba, wanda ta ce hakan na matukar dakile ci gaban yankin. Sai dai ta ja hankalin matan da cewa duk wacce ta samu dama to ta zama mai kare mutucinta, domin a cewarta; “kare mutunci na da matukar amfani”.

 

Har wala yau a wani bangare na bayaninta, ta yi tilawar yadda ta rika bai wa mijinta shawarwari wadanda a karshe suka taimaki al’umma da kasarnan. A nan ne ta jawo hankalin mata da cewa; akwai bukatar su rika taimakon mazajensu ta hanyar ba su shawarwari da bayanai da za su taimakawa mazajensu da al’umma baki daya.

 

Sannan ta ja hankalin mazan da cewa yakamata a bangarensu su rika jin shawarwarin matansu, wanda ta ce idan miji na sauraren shawarwarin matarsa, tabbas zai amfane shi; “na sha bai wa maigida shawara, kuma ya dauka ya amfanar da kasa”, ta jaddada. Ta kara da cewa; “yana da kyau mace ta shiga aikin mijinta domin kawo gyara wanda zai amfani al’umma”, ta lurantar.

 

Sannan ta janyo hankalin al’umma cewa duk wanda ya samu kansa a wani matsayi ko mukami, to ya tabbata ya hidimtawa al’umma kuma ka da ka kasance mai danne na kasa da kai, domin a cewarta rayuwa na sauyawa. Inda ta ce; “Rayuwa yana da kyau idan ka samu dama; kudi ko mulki, ka yi adalci, kirki da kuma gaskiya. Rayuwa wucewa take yi”.

 

Har wala yau ta shaidawa ‘yan jaridar cewa; duk wani aiki da mutum ya kuduri aniyarsa ya yi shi da kyakkyawan niyya, “tabbas Allah zai taimake shi”, inji ta.

 

Sannan ta ja hankalin mata da su rika bibiyar tarihin wadanda suka gabace su domin fahimtar kura-kuran da suka yi domin su kuma su dauki darasi. Ta ce akwai bukatar mata su rika daukar darussa na rayuwa.

 

Hajiya (Dr) Maryam Abacha har wala yau a bayaninta ta zayyano irin ci gaban da ta samar a lokacin da ta rike shugabancin kungiyar matan ofisoshi sojoji wato NAOWA da kuma zuwa lokacin da ta zama Uwargidan shugaban kasa. A yayin da ta rike shugabancin NAOWA, ta samar da dimbin shirye-shirye na tallafawa sojoji da matan sojoji ta hanyar ilmantar da ‘ya’yansu, koyawa mata sana’o’i da kuma ba su tallafi. Baya ga haka, ta kafa kungiyar hadaka ta matan sojoji da ‘yan sanda wato JOFOPOWOCCO wacce daga baya aka sauya wa kungiyar suna zuwa DEPOWA, wato kungiyar matan hafsoshin tsaro da ‘yan sanda domin kyautata alakar dake tsakanin fadar shugaban kasa da kuma wadannan rassan tsaro.

 

Daga cikin dimbin nasarorin da ta samarwa da Nijeriya a yayin da take rike ofishin Uwargidan shugaban kasa, sun hada da; shirin tallafawa iyali; shiri da ke tallafawa iyali a bangaren ilimi, lafiya, noma da kiwo, samar da kudaden shiga, tallafawa gajiyayyu da sauran su. Sannan ta samar da shirin ci gaban tattalin arzikin iyali, shirin allurar rigakafi ta kasa, shiriin tallafawa masu bukatar shigar da kara gaban shari’a, asibitin kasa na mata da kananan yara, bayar da gudummawa ga fadar shugaban kasa, shirin gwamnati, samar da ofishin tuntuba na tsoffin shugaban kasa da iyalinsu da sauran su.

 

Baya ga haka, a bangaren lafiya ta kirkiro shirin yakar cutar kanjamau da kuma na allurar rigakafi ga kananan yara. Wanda shiri ne da aka bullo da shi domin yakar cututtuka shida da suka fi addabar yara a wancan lokacin. Saboda irin wannan gudummawar da ta bayar hukumar lafiya ta duniya ta nada ta a matsayin Jakadiyyar kawar da cutar foliyo a Afrika.

 

Uwargidan shugaban kasa, Hajiya Maryam Abacha bisa shawararta aka samar da ma’aikatar lura da harkokin mata da ci gaban zamantakewa a 1995.

Abacha
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.