ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Na Da Rawar Da Za Su Taka Wajen Ci Gaban Al’umma Idan Aka Ba Su Dama – Maryam Abacha

by Bello Hamza
3 years ago
Abacha

Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Marigayi Janar Sani Abacha, wato Hajiya (Dr) Maryam Abacha ta ja hankalin al’umma musamman mazaje da su rika bai wa mata dukkanin wata dama da ‘yanci na neman ilimi da aiki ko sana’a domin ci gaban al’umma baki daya.

 

Dr Maryam Abacha ta bayyana hakan ne a ranar Talata a yayin da take ganawa da manema labarai a gidanta dake birnin Tarayya Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

Hajiya Maryam ta ce mata suna da tasirin gaske wajen gina ingantacciyar al’umma, domin su ke tarbiyyar al’umma, inda ta yi amfani da wannan dama wajen kira na musamman ga mazaje da su rika bai wa matansu dama ta neman ilimi da aiki ko sana’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Dr Maryam ta ce maza musamman a arewacin Nijeriya ba su cika taimakawa matansu wajen cimma burinsu ba, wanda ta ce hakan na matukar dakile ci gaban yankin. Sai dai ta ja hankalin matan da cewa duk wacce ta samu dama to ta zama mai kare mutucinta, domin a cewarta; “kare mutunci na da matukar amfani”.

 

Har wala yau a wani bangare na bayaninta, ta yi tilawar yadda ta rika bai wa mijinta shawarwari wadanda a karshe suka taimaki al’umma da kasarnan. A nan ne ta jawo hankalin mata da cewa; akwai bukatar su rika taimakon mazajensu ta hanyar ba su shawarwari da bayanai da za su taimakawa mazajensu da al’umma baki daya.

 

Sannan ta ja hankalin mazan da cewa yakamata a bangarensu su rika jin shawarwarin matansu, wanda ta ce idan miji na sauraren shawarwarin matarsa, tabbas zai amfane shi; “na sha bai wa maigida shawara, kuma ya dauka ya amfanar da kasa”, ta jaddada. Ta kara da cewa; “yana da kyau mace ta shiga aikin mijinta domin kawo gyara wanda zai amfani al’umma”, ta lurantar.

 

Sannan ta janyo hankalin al’umma cewa duk wanda ya samu kansa a wani matsayi ko mukami, to ya tabbata ya hidimtawa al’umma kuma ka da ka kasance mai danne na kasa da kai, domin a cewarta rayuwa na sauyawa. Inda ta ce; “Rayuwa yana da kyau idan ka samu dama; kudi ko mulki, ka yi adalci, kirki da kuma gaskiya. Rayuwa wucewa take yi”.

 

Har wala yau ta shaidawa ‘yan jaridar cewa; duk wani aiki da mutum ya kuduri aniyarsa ya yi shi da kyakkyawan niyya, “tabbas Allah zai taimake shi”, inji ta.

 

Sannan ta ja hankalin mata da su rika bibiyar tarihin wadanda suka gabace su domin fahimtar kura-kuran da suka yi domin su kuma su dauki darasi. Ta ce akwai bukatar mata su rika daukar darussa na rayuwa.

 

Hajiya (Dr) Maryam Abacha har wala yau a bayaninta ta zayyano irin ci gaban da ta samar a lokacin da ta rike shugabancin kungiyar matan ofisoshi sojoji wato NAOWA da kuma zuwa lokacin da ta zama Uwargidan shugaban kasa. A yayin da ta rike shugabancin NAOWA, ta samar da dimbin shirye-shirye na tallafawa sojoji da matan sojoji ta hanyar ilmantar da ‘ya’yansu, koyawa mata sana’o’i da kuma ba su tallafi. Baya ga haka, ta kafa kungiyar hadaka ta matan sojoji da ‘yan sanda wato JOFOPOWOCCO wacce daga baya aka sauya wa kungiyar suna zuwa DEPOWA, wato kungiyar matan hafsoshin tsaro da ‘yan sanda domin kyautata alakar dake tsakanin fadar shugaban kasa da kuma wadannan rassan tsaro.

 

Daga cikin dimbin nasarorin da ta samarwa da Nijeriya a yayin da take rike ofishin Uwargidan shugaban kasa, sun hada da; shirin tallafawa iyali; shiri da ke tallafawa iyali a bangaren ilimi, lafiya, noma da kiwo, samar da kudaden shiga, tallafawa gajiyayyu da sauran su. Sannan ta samar da shirin ci gaban tattalin arzikin iyali, shirin allurar rigakafi ta kasa, shiriin tallafawa masu bukatar shigar da kara gaban shari’a, asibitin kasa na mata da kananan yara, bayar da gudummawa ga fadar shugaban kasa, shirin gwamnati, samar da ofishin tuntuba na tsoffin shugaban kasa da iyalinsu da sauran su.

 

Baya ga haka, a bangaren lafiya ta kirkiro shirin yakar cutar kanjamau da kuma na allurar rigakafi ga kananan yara. Wanda shiri ne da aka bullo da shi domin yakar cututtuka shida da suka fi addabar yara a wancan lokacin. Saboda irin wannan gudummawar da ta bayar hukumar lafiya ta duniya ta nada ta a matsayin Jakadiyyar kawar da cutar foliyo a Afrika.

 

Uwargidan shugaban kasa, Hajiya Maryam Abacha bisa shawararta aka samar da ma’aikatar lura da harkokin mata da ci gaban zamantakewa a 1995.

Abacha
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.