ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Na Da Rawar Da Za Su Taka Wajen Ci Gaban Al’umma Idan Aka Ba Su Dama – Maryam Abacha

by Bello Hamza
3 years ago
Abacha

Uwargidan tsohon shugaban Nijeriya, Marigayi Janar Sani Abacha, wato Hajiya (Dr) Maryam Abacha ta ja hankalin al’umma musamman mazaje da su rika bai wa mata dukkanin wata dama da ‘yanci na neman ilimi da aiki ko sana’a domin ci gaban al’umma baki daya.

 

Dr Maryam Abacha ta bayyana hakan ne a ranar Talata a yayin da take ganawa da manema labarai a gidanta dake birnin Tarayya Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

Hajiya Maryam ta ce mata suna da tasirin gaske wajen gina ingantacciyar al’umma, domin su ke tarbiyyar al’umma, inda ta yi amfani da wannan dama wajen kira na musamman ga mazaje da su rika bai wa matansu dama ta neman ilimi da aiki ko sana’a.

 

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Dr Maryam ta ce maza musamman a arewacin Nijeriya ba su cika taimakawa matansu wajen cimma burinsu ba, wanda ta ce hakan na matukar dakile ci gaban yankin. Sai dai ta ja hankalin matan da cewa duk wacce ta samu dama to ta zama mai kare mutucinta, domin a cewarta; “kare mutunci na da matukar amfani”.

 

Har wala yau a wani bangare na bayaninta, ta yi tilawar yadda ta rika bai wa mijinta shawarwari wadanda a karshe suka taimaki al’umma da kasarnan. A nan ne ta jawo hankalin mata da cewa; akwai bukatar su rika taimakon mazajensu ta hanyar ba su shawarwari da bayanai da za su taimakawa mazajensu da al’umma baki daya.

 

Sannan ta ja hankalin mazan da cewa yakamata a bangarensu su rika jin shawarwarin matansu, wanda ta ce idan miji na sauraren shawarwarin matarsa, tabbas zai amfane shi; “na sha bai wa maigida shawara, kuma ya dauka ya amfanar da kasa”, ta jaddada. Ta kara da cewa; “yana da kyau mace ta shiga aikin mijinta domin kawo gyara wanda zai amfani al’umma”, ta lurantar.

 

Sannan ta janyo hankalin al’umma cewa duk wanda ya samu kansa a wani matsayi ko mukami, to ya tabbata ya hidimtawa al’umma kuma ka da ka kasance mai danne na kasa da kai, domin a cewarta rayuwa na sauyawa. Inda ta ce; “Rayuwa yana da kyau idan ka samu dama; kudi ko mulki, ka yi adalci, kirki da kuma gaskiya. Rayuwa wucewa take yi”.

 

Har wala yau ta shaidawa ‘yan jaridar cewa; duk wani aiki da mutum ya kuduri aniyarsa ya yi shi da kyakkyawan niyya, “tabbas Allah zai taimake shi”, inji ta.

 

Sannan ta ja hankalin mata da su rika bibiyar tarihin wadanda suka gabace su domin fahimtar kura-kuran da suka yi domin su kuma su dauki darasi. Ta ce akwai bukatar mata su rika daukar darussa na rayuwa.

 

Hajiya (Dr) Maryam Abacha har wala yau a bayaninta ta zayyano irin ci gaban da ta samar a lokacin da ta rike shugabancin kungiyar matan ofisoshi sojoji wato NAOWA da kuma zuwa lokacin da ta zama Uwargidan shugaban kasa. A yayin da ta rike shugabancin NAOWA, ta samar da dimbin shirye-shirye na tallafawa sojoji da matan sojoji ta hanyar ilmantar da ‘ya’yansu, koyawa mata sana’o’i da kuma ba su tallafi. Baya ga haka, ta kafa kungiyar hadaka ta matan sojoji da ‘yan sanda wato JOFOPOWOCCO wacce daga baya aka sauya wa kungiyar suna zuwa DEPOWA, wato kungiyar matan hafsoshin tsaro da ‘yan sanda domin kyautata alakar dake tsakanin fadar shugaban kasa da kuma wadannan rassan tsaro.

 

Daga cikin dimbin nasarorin da ta samarwa da Nijeriya a yayin da take rike ofishin Uwargidan shugaban kasa, sun hada da; shirin tallafawa iyali; shiri da ke tallafawa iyali a bangaren ilimi, lafiya, noma da kiwo, samar da kudaden shiga, tallafawa gajiyayyu da sauran su. Sannan ta samar da shirin ci gaban tattalin arzikin iyali, shirin allurar rigakafi ta kasa, shiriin tallafawa masu bukatar shigar da kara gaban shari’a, asibitin kasa na mata da kananan yara, bayar da gudummawa ga fadar shugaban kasa, shirin gwamnati, samar da ofishin tuntuba na tsoffin shugaban kasa da iyalinsu da sauran su.

 

Baya ga haka, a bangaren lafiya ta kirkiro shirin yakar cutar kanjamau da kuma na allurar rigakafi ga kananan yara. Wanda shiri ne da aka bullo da shi domin yakar cututtuka shida da suka fi addabar yara a wancan lokacin. Saboda irin wannan gudummawar da ta bayar hukumar lafiya ta duniya ta nada ta a matsayin Jakadiyyar kawar da cutar foliyo a Afrika.

 

Uwargidan shugaban kasa, Hajiya Maryam Abacha bisa shawararta aka samar da ma’aikatar lura da harkokin mata da ci gaban zamantakewa a 1995.

Abacha
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.