ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canjin Kudi: Dole Ne Mu Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa —Matawalle

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamna Bello Matawalle na Jihar Zamfara, ya ce shi da takwarorinsa sun kai Gwamnatin Tarayya gaban kotun koli ne domin ceto tattalin arzikin kasar nan daga durkushewa.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya bayar da rahoton cewa, gwamnoni uku na jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara sun maka gwamnatin tarayya a kotun koli, inda suke neman ta dakatar da shirin sauya fasalin Naira na Babban Bankin Nijeriya (CBN).

  • Mata Na Da Rawar Da Za Su Taka Wajen Ci Gaban Al’umma Idan Aka Ba Su Dama – Maryam Abacha
  • Da ɗumi-ɗuminsa: Mataimakin Gwamnan Sakkwato Ya Koma APC

NAN ya kuma ruwaito cewa a ranar Laraba ne kotun koli ta dakatar da CBN daga aiwatar da wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu na daina amfani tsofaffin takardun kudi.

ADVERTISEMENT

Wata sanarwa da aka fitar a Gusau a ranar Alhamis, ta hannun mai ba shi shawara ta musamman kan wayar da kan jama’a da yada labarai da sadarwa, Malam Zailani Bappa, ta ce wadanda suka yi adawa da matakin da suka dauka da nasarar da suka samu a kotun koli sun yi kuskure.

“Bayan kalaman rashin gaskiya da ke biyo bayan hukuncin da Kotun Koli ta kasa ta yanke na saurare da kuma aiwatar da bukatar gwamnonin da suka yi nasara a kan musayar Naira, Matawalle ya bayyana ra’ayinsu a matsayin siyasa kawai.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Na tabbata cewa wadanda suka yi adawa da matakin da muka dauka na Kotun Koli ko dai sun rude ne ko kuma sun makantar da su saboda son zuciya.

“Ni da takwarorina na jihohin Kaduna da Kogi mun ga ya dace mu tunkari kotun koli domin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga fadawa cikin mawuyacin hali.

“Kuma don kawar da radadin da talakawan Nijeriya ke fama da shi ta fuskar karancin kudi na tsofaffi da sabbin kudin Naira,” in ji Matawalle.

A cewarsa, yana da kyau a ce dole ne CBN da bankunan kasuwanci su samar da sabbin takardun Naira domin gudanar da harkokin kasuwanci na yau da kullum kafin a ayyana daina amfani da tsofaffin takardun kudi.

Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa da kalaman abokan hamayyarsa na siyasa, inda ya kara da cewa jam’iyyun siyasar da ke kalubalantar hukuncin kotun ba su da muradin kasar nan a zuciya.

“Hukuncin da alkalan kotun koli masu hikima da mutuntawa suka yanke kan wannan lamari, ita ce hanya mafi dacewa don magance matsalar da ake fama da ita da kuma sakamakon da ke tafe a halin yanzu.”

Matawalle ya kara da cewa, “A wannan mawuyacin lokaci na mika mulki, kishin kasa ne kawai ke gabanmu, mu ajiye tunanin siyasa a gefe tare da magance kalubalen da ke gabanmu.”

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.