ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canjin Kudi: Dole Ne Mu Ceto Tattalin Arzikin Nijeriya Daga Durkushewa —Matawalle

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamna Bello Matawalle na Jihar Zamfara, ya ce shi da takwarorinsa sun kai Gwamnatin Tarayya gaban kotun koli ne domin ceto tattalin arzikin kasar nan daga durkushewa.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya bayar da rahoton cewa, gwamnoni uku na jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara sun maka gwamnatin tarayya a kotun koli, inda suke neman ta dakatar da shirin sauya fasalin Naira na Babban Bankin Nijeriya (CBN).

  • Mata Na Da Rawar Da Za Su Taka Wajen Ci Gaban Al’umma Idan Aka Ba Su Dama – Maryam Abacha
  • Da ɗumi-ɗuminsa: Mataimakin Gwamnan Sakkwato Ya Koma APC

NAN ya kuma ruwaito cewa a ranar Laraba ne kotun koli ta dakatar da CBN daga aiwatar da wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu na daina amfani tsofaffin takardun kudi.

ADVERTISEMENT

Wata sanarwa da aka fitar a Gusau a ranar Alhamis, ta hannun mai ba shi shawara ta musamman kan wayar da kan jama’a da yada labarai da sadarwa, Malam Zailani Bappa, ta ce wadanda suka yi adawa da matakin da suka dauka da nasarar da suka samu a kotun koli sun yi kuskure.

“Bayan kalaman rashin gaskiya da ke biyo bayan hukuncin da Kotun Koli ta kasa ta yanke na saurare da kuma aiwatar da bukatar gwamnonin da suka yi nasara a kan musayar Naira, Matawalle ya bayyana ra’ayinsu a matsayin siyasa kawai.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Na tabbata cewa wadanda suka yi adawa da matakin da muka dauka na Kotun Koli ko dai sun rude ne ko kuma sun makantar da su saboda son zuciya.

“Ni da takwarorina na jihohin Kaduna da Kogi mun ga ya dace mu tunkari kotun koli domin ceto tattalin arzikin Nijeriya daga fadawa cikin mawuyacin hali.

“Kuma don kawar da radadin da talakawan Nijeriya ke fama da shi ta fuskar karancin kudi na tsofaffi da sabbin kudin Naira,” in ji Matawalle.

A cewarsa, yana da kyau a ce dole ne CBN da bankunan kasuwanci su samar da sabbin takardun Naira domin gudanar da harkokin kasuwanci na yau da kullum kafin a ayyana daina amfani da tsofaffin takardun kudi.

Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa da kalaman abokan hamayyarsa na siyasa, inda ya kara da cewa jam’iyyun siyasar da ke kalubalantar hukuncin kotun ba su da muradin kasar nan a zuciya.

“Hukuncin da alkalan kotun koli masu hikima da mutuntawa suka yanke kan wannan lamari, ita ce hanya mafi dacewa don magance matsalar da ake fama da ita da kuma sakamakon da ke tafe a halin yanzu.”

Matawalle ya kara da cewa, “A wannan mawuyacin lokaci na mika mulki, kishin kasa ne kawai ke gabanmu, mu ajiye tunanin siyasa a gefe tare da magance kalubalen da ke gabanmu.”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

Buhari Ya Nada Farfesa Magaji, Sabon Shugaban Kwalejin Fasaha Ta Kasa Da Ke Kabo, Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.