• Leadership Hausa
Saturday, March 25, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Amai Da Gudawa Ta Bulla A Kano

by Sadiq
9 months ago
in Labarai
0
Cutar Amai Da Gudawa Ta Bulla A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar Lafiya Ta Jihar Kano ta tabbatar da bullar cutar amai da gudawa a birnin Kano.

Babban jami’in kula da cututtuka masu yaduwa na ma’aikatar, Sulaiman Iliyasu ne, ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano.

  • 2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi
  • Badakalar Kudin Makamai: PDP Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Buratai

Ya ce an samu rahoton bullar cutar a karamar hukumar Danbatta wadda har aka samu asarar rayukan mutane biyu.

“A watan Afrilu mun samu rahoton bullar cutar amai da gudawa a Danbatta wadda daga nan kuma sai cutar ta bulla a karamar hukumar Gwarzo”.

Dakta Iliyasu ya ce “Ya zuwa yanzu sama da mutane 25 zuwa 30 ne suka kamu da cutar a kwaryar birnin Kano kamar yadda sakamakon gwajin da muka yi ya tabbatar”.

Labarai Masu Nasaba

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

A cewarsa yanzu haka kananan hukumomin da suka samu ɓullar cutar sun haɗa da karamar hukumar Dala, Ungoggo, karamar hukumar Birni da kuma Tarauni.

Sai dai ya bukaci al’umma da su kara kula da tsaftar muhallansu da kuma kai rahoton duk wata cuta da ta bulla ga hukumomin lafiya don daukar matakin gaggawa.

Ita dai cutar amai da gudawa wadda ake kira Kwalara, na bulla ne a sanadin rashin tsaftace muhalli kama daga kan abinci da ake ci zuwa gyaran jiki da sauransu.

Idan mutum ya kamu ya kan dinga yin amai ko gudawa, a wasu lokutan ma duka biyun har ta kai ga mutum ya galabaita idan ba a ba shi kulawa a kan lokaci ba.

Tags: Amai Da GudawaDamnbattakanoKwalaraMa'aikatar LafiyaRashin LafiyaTarauniUngogo
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi

Next Post

Kalvin Phillips Ya Koma Manchester City Daga Leeds United

Related

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC
Labarai

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

3 mins ago
Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano
Labarai

Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

2 hours ago
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi
Manyan Labarai

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

4 hours ago
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman
Labarai

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

5 hours ago
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari
Manyan Labarai

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

6 hours ago
INEC Ta Yi Mun Daidai Da Ta Ayyana Zaɓen Gwamnan Adamawa Bai Kammalu Ba – Binani
Labarai

INEC Ta Yi Mun Daidai Da Ta Ayyana Zaɓen Gwamnan Adamawa Bai Kammalu Ba – Binani

6 hours ago
Next Post
Kalvin Phillips Ya Koma Manchester City Daga Leeds United

Kalvin Phillips Ya Koma Manchester City Daga Leeds United

LABARAI MASU NASABA

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

March 25, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 4

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 4

March 25, 2023
An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

March 25, 2023
Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

March 25, 2023
Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

March 25, 2023
An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

March 25, 2023
Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

March 25, 2023
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

March 25, 2023
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

March 25, 2023
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

March 25, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.