• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Goje Daga Jam’iyyar Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Goje Daga Jam’iyyar Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin jam’iyyar APC na gundumar Kashere da ke karamar hukumar Akko a Jihar Gombe, sun kori Sanata mai wakiltar Gombe ta tsakiya, Danjuma Goje, bisa zargin yi mata zagon kasa.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a kwanakin baya ne jam’iyyar a matakin Kashere ta kafa wani kwamiti da zai binciki zargin cin mutuncin jam’iyyar da tsohon gwamnan jihar, a lokacin zaben 2023 da aka kammala.

  • Binani Ta Shigar Da Kara Kotu Kan Bukatar Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zabe
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Direba A Ondo

Da yake jawabi ga manema labarai a garin Kashere, shugaban jam’iyyar APC na yankin, Tanimu Abdullahi, ya bayyana cewa jam’iyyar ta dauki matakin korar Goje baki daya ne bayan ta same shi da laifukan cin mutuncin jam’iyyar da rashin halartar taron yakin neman zaben jam’iyyar APC a Jihar Gombe wanda jam’iyyar ta kasa ta jagoranta.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Sanata Abdullahi Adamu, ya kara da cewa, ana kuma zargin Sanatan da kauracewa duk wani rangadin yakin neman zaben jam’iyyar a shiyyarsa.

“Kwamitin ya kuma tattauna kan zargin da ake yi wa Goje na yi wa jam’iyyun adawa aiki da ‘yan takararsu da nufin kawo cikas ga nasarar jam’iyyar APC a Jihar Gombe da ma Nijeriya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ya kara da cewa, “Bayan goyon baya ga ‘yan takarar jam’iyyar adawa ta hanyar karbar dan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar NNPP da kuma dan takarar majalisar wakilai ta tarayya a jam’iyyar PDP Akko a gidansa tare da bayar da goyon baya ga jam’iyyarsa ta APC da sauran al’amura da dama.

Abdullahi ya ci gaba da cewa, wasu laifukan da Sanata Goje ya aikata sun hada da “kawo cikas ga gwamnatin APC a jihar da kuma daukar nauyin yakin neman zabe da nufin tunzura jama’a kan gwamnatin APC a jihar.

“Bayar da takamaiman umarni ga abokansa da jami’an tsaronsa da su ki yin aiki da manufar jam’iyyar APC a Jihar Gombe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGombeSanata GojeZagon Kasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binani Ta Shigar Da Kara Kotu Kan Bukatar Ayyana Ta A Matsayin Wadda Ta Lashe Zabe

Next Post

Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

Related

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

3 weeks ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 weeks ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

4 weeks ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

1 month ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

2 months ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

2 months ago
Next Post
Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.