• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

by Bello Hamza and Sulaiman
3 months ago
Dangote

Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya jinjinawa Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA.

Dangote, ya yabawa NPA ne, bisa kokarinta na wanzar da tsarin Gwamnatin Tarayya na sayar da Danyen Mai da kuma Man Fetur, da sauran dangogin Man Fetur da ake tacewa a cikin gida Nijeriya, kan farashin Naira.

  • Al’umma Na Kokawa Kan Tsadar Kayan Miya A Sassan Kasar Nan
  • Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

A saboda hakan ne, Dangote, ya bayar da kyautar sabuwar motar Bas kirar Coaster, domin karfafawa kwamitin da zai aikin, guiwa, wanda a turance, ake kira da One-Stop-Shop.

A cikin wata wasika da Dangote ya rattabawa hannu, ya kuma bayar da tabbcin cewa, Kamfaninsa zai ci gaba da samar da hanyoyin da zai rinka taimakwa kwamntin, domin ya samu gudanar da aikin da aka dora masa, bisa umarnin Fadar Shugaban kasa.

“Mun ammana da cewa, wannan motar Bas din, kwamitin zai yi aiki da ita yadda ya kamata, duba da cewa, Kamfanin na, zai ci gaba da bai wa kwamtin goyon baya,” Inji Dangote.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

Idan za a iya tunawa, Shugaban karamin kwamitin na wanzar da sayar da Danyen Man da kuma sauran dangogin Man Fetur da ake tacewa kasar kan farashin Naira Zacch Adedeji, ya jabawa hukumar ta NPA, bisa samar da aikin a cikin sauki

Adedeji, ya yi wannan yabon ne, lokacin da ya jagoranci tawagar kwamtin zuwa hukumar ta NPA, inda kuma ya yabawa tawagar kwamtin, da ke a karkashin NPA, kan gundunmawar da take ci gaba da bayar wa, domin a samu cimma burin da aka sanya a gaba.

“Mun lura da cewa, babu shakka wannan kokarin na hukumar ta NPA ya nuna irin kishin da hukumar take da shi a zahir, wajen cimma nasarar da aka sanya a gaba, “A cewar Adedeji.

“Ina mai kara maku kwarin guiwar cewa, kar ku gajiya wajen cimma burin da aka sanya a gaba, musamman domin a samu cin nasarar aikin, kuma muna mika godiyar mu, ga sauran hukumomin da suke ci gaba da bayar da goyon bayansu”. In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 
Tattalin Arziki

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Next Post
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Gaza

Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar

October 12, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

October 12, 2025
‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

October 12, 2025
Yadda Ake Gurasa Ta Semovita

Yadda Ake Gurasa Ta Semovita

October 12, 2025
Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

October 12, 2025
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

October 12, 2025
Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

October 12, 2025
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

October 12, 2025
Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.