ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadace-Fadacen Daba A Birnin Kano: Ina Mafita?

by Leadership Hausa
2 years ago
Daba

Rikicin Daba a cikin birnin Kano da wasu gefunan birnin ba sabon abu ba ne, za mu iya cewa abu ne da ya ki ci ya ki cinyewa, wato matsala ce ta shekara da shekaru, wanda sanadiyyar hakan rayukan al’ummomi sun salwanta, kama daga ‘yan ba ruwa na da Dukiyoyi jama’a. A inda a wasu lokutan hatta Hukumomin Tsaro ba su tsira daga farmakin rasa rai ba.

Wannan muguwar dabi’a ta Daba zuwa yanzu dai tana son ta zamo kamar wutar daji duba da yadda kullum take ta samun guraben zama a ciki da kauyukan Kano, duk da hukumomin tsaro suna ta ikirarin magance matsalar, da dai-daikun kungiyoyin sakai.

  • 2023: Manyan Jiragen Ruwa 75,000 Suka Yi Hada-hada A Tashar Lekki
  • Yadda Dangote Ya Raba Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 15, Jihar Kano Ta Samu Kaso Mafi Tsoka

Babban Abun tashin hankali shi ne yadda unguwanni da dama za ka ga yadda suke kokarin kafa kungiyoyin Sa-kai dan tunkara ko kuma magance matsalar tsaro daga tushe amma har zuwa yanzu babu wani kyakkyawan sakamako, in muka iy la’akari da yadda Dabar ke kara bunkasa tare da canja salo a Jihar ta Kano da kuma samun guraben zama.

ADVERTISEMENT

Mafuta: Akwai Bukatar Duk wata unguwa da suke fuskantar irin wannan matsalolin na tsaro da su tashi su yi aiki tuKuru wajen shigo da kowa cikin aikin samar da tsaro Kama daga kan Masu unguwanni, Limamai, Malamai Na Addini da ‘yan takarda da Kungiyoyin Matasa da na dalibai har da dai-dai kun jama’ar unguwa ko yanki. Domin tsaro na kowa ne, duk inda aka rasa tsaro to lallai za a rasa Aminci da walwala a wannan guri. Haka kuma dole sai an rufe Ido tare da tursasa wa dai-daikun mutanen da za su kawo tasgaro a cikin tsarin ta fuskar alakarsu da yaran da suke aikata wannan dabi’u. Haka kuma sai an yaki miyagun kwayoyi tare da saka idanuwa a shagunan sayar da magunguna.

Sannan a yi kokarin ba wa masu sana’a a kan hanyoyin shige da ficen jama’a wani horo da za su na saka idanuwa kan shige da ficen bakin fuska a kowanne yanki, tare da ba da bayanan sirri na faruwar duk wani motsi ko abu wanda zai kai ga barazana da rayuwa ko salwantar Dukiyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Abun Lura: Dole Yayin Gudanar Da Wannan Aiki Sai An cire
1). Tsoro: Kowa ya ji cewa rai daya yake zai iya badawa wajen tunkarar yaran da suke hana iyaye, kanne, maza da mata da kasuwancin unguwa zaman lafiya, uwa uba gudanar da ibadoji, tare da tunkarar kalubale kan iyayen yaran da za su ki bada hadinkai kasancewar ‘yayansu ne ko kanne ko yayye ke aikata wadannan ayyukan na ta’addanci a unguwanni.
2). Wariya: Wato cewa ni ai bai shafe ni ba sai a bar wa wane da wane.
3). Bangaranci: Ma’ana ai ni ba a yi a yankin da nake ba, to ka sani tsaro na kowa ne.
Allah Ka amintar da Unguwanninmu, da garuruwanmu ka ba mu lafiya da zama lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko

Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.