• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kaudar tumatur na daga cikin hanyar da manoma kan bi wajen adana tumaturi domin yin amfani da shi a lokacin da babau danye, musamman a lokacin bazara ko kuma tsakiyar damuna.

Akwai wurare daban-daban da ake noman tumatur a fadin kasar nan a lokacin rani, Kwanar-gafan da ke karamar hukumar Garun-malam, a jihar Kano na daga cikin manyan kasuwannin tumatur a fadin kasar nan, wadda ake zuwa daga sassa daban-daban domin yin kasuwcin tumaturin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance
  • Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

Ana kai tumaturin zuwa sassa daban-daban na kasar nan, har ma zuwa makotanmu. Manoman wannan yanki na kai tumaturin nasu wannan kasuwa, domin su sayar.

Kasuwar na daga cikin kasuwannanin da ke samar da hada-hadar kasuwanci ga dimbin al’umma daga sassa daban-daban na kasar nan.

Bayan hada-hadar kasuwancin danyen tumaturin akwai wadanda ke hada-hadar kasuwancin kaudarsa, wato busasshensa ke nan.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Mayar da tumaturin zuwa kauda na taimaka wa manomansa rage asara, musamman idan suka daure, suka adana shi zuwa wani lokaci,wato, lokacin farkon damuna, kafin na damuna ya fara shigo wa.

Sai dai duk da haka, a kan yi hada-hadar kasuwancin kaudar tumaturin tun daga lokacin da aka fara shanya shi.

A bana musamman halin da aka shiga na sauyin kudi, ya dakile kasuwar tumatur yadda manomansa suka yi dimbin asara. Masu nomansa da masu kasuwancinsa sun shiga halin tsaka-mai-wuya, saboda matsalar kudin da za yi amfani da su wajen yin safarar ta sa. Wannan ta sa dole manoman suka shiga shanya tumaturin nasu, tunda babu kasuwa.

A makwanni biyu da suka wuce a kasuwar kwanan-gafan babbar kasuwar tumaturin ta Kwanar-gafan kasuwar tunatur ta fadi kasa warwas, inda manoma ke sayar da katon Kwando a kan naira dubu biyu zuwa naira dubu biyu da dari biyar, wannan ta sa yawan masu shanyarsa ya karu. Karuwar masu shanyar ta sa farashin busassahen tumaturin ya fadi kasa warwas.

Duk da cewa, a daidai wannan loacin, lokaci ne na ganiyar samun kaudar tumaturin, kuma yakan yi sauki matuka, wanda har masu sari kan saya su adana shi, to amma a bana faduwar farashin ta yi kasa sosai, saboda wanda yakamata a sayar da shi kuma a yi amfani da shi tun yana danye, yanayi ya sa hakan ba ta yiwu ba.

Manoman tumarurin dai sun koka matuka da faduwar farashin, domin yana taimaka musu wajen samun kudaden yin hidimarsau ta yau da kullum.

Sannan kuma yana taimaka wa manoman wajen yin noman damuna. Saboda haka a bana manoman na tumatur da masu kasuwancin busassahen tumaturin sun shiga halin tsaka-mai-wuya.

Sannan kuma a daidai wannan lokacin da ake sanyi, yawan tumarun da ake diba na karuwa. Ga yawa na karuwa ga farashi na sauka.

Sai dai wani manomi da aka zanta da shi, a kasuwar ta Kwanar-gafan ya tabbatar da cewa, faduwar farashin kaudar tumaturin zai shafi noman damina, domin kudin da suke samu daga noman tumatirin ya ragu kwarai.

Sannan kuma wasu manoman sun bukaci gwamnati da manyan ‘yan kasuwa da su taimaka musu wajen kafa musu masana’antar da za ta sarrafa tumaturin yadda za a iya adana shi, da kuma daukarsa a kai shi sassa daban-daban na ciki da wajen kasar nan. Domin kuwa yin hakan zai taimaka musu wajen rage asarar da suke fuskanta a halin yanzu.

Wani mai kasuwancin kaudar tumaturin da ke zaune a garin Kwanar-dangora, mai suna Sani Bilak, ya koka matuka kan yadda a bana hada-hadar kasuwancin ta su ta samu cikas, wanda ya ce, hakan ta kawo musu cikas matuka.

Don haka, shi ma kiran da nasa ga gwamnati ya yi da manyana ‘yan kasuwa da su samar da hanyar da za a dinga adana tumaturin domin guje wa irin wannan mummunar asara.

Masu shanyar kaudar tumaturin su ma sun ce da gwamnati za ta tallafa musu wajen samar musu da na’urar da za ta busar da tumaturin da an samu saukin yawan asarar da ake yi, sannan kuma zai kasance yana da tsafta, amma a halin yanzu ana sanya shi a wuraen da ba su dace ba. Inda babu cikakkiyar tsafta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarashiTumatir
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara

Next Post

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

1 day ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

1 day ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.