• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kaudar tumatur na daga cikin hanyar da manoma kan bi wajen adana tumaturi domin yin amfani da shi a lokacin da babau danye, musamman a lokacin bazara ko kuma tsakiyar damuna.

Akwai wurare daban-daban da ake noman tumatur a fadin kasar nan a lokacin rani, Kwanar-gafan da ke karamar hukumar Garun-malam, a jihar Kano na daga cikin manyan kasuwannin tumatur a fadin kasar nan, wadda ake zuwa daga sassa daban-daban domin yin kasuwcin tumaturin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance
  • Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

Ana kai tumaturin zuwa sassa daban-daban na kasar nan, har ma zuwa makotanmu. Manoman wannan yanki na kai tumaturin nasu wannan kasuwa, domin su sayar.

Kasuwar na daga cikin kasuwannanin da ke samar da hada-hadar kasuwanci ga dimbin al’umma daga sassa daban-daban na kasar nan.

Bayan hada-hadar kasuwancin danyen tumaturin akwai wadanda ke hada-hadar kasuwancin kaudarsa, wato busasshensa ke nan.

Labarai Masu Nasaba

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

Mayar da tumaturin zuwa kauda na taimaka wa manomansa rage asara, musamman idan suka daure, suka adana shi zuwa wani lokaci,wato, lokacin farkon damuna, kafin na damuna ya fara shigo wa.

Sai dai duk da haka, a kan yi hada-hadar kasuwancin kaudar tumaturin tun daga lokacin da aka fara shanya shi.

A bana musamman halin da aka shiga na sauyin kudi, ya dakile kasuwar tumatur yadda manomansa suka yi dimbin asara. Masu nomansa da masu kasuwancinsa sun shiga halin tsaka-mai-wuya, saboda matsalar kudin da za yi amfani da su wajen yin safarar ta sa. Wannan ta sa dole manoman suka shiga shanya tumaturin nasu, tunda babu kasuwa.

A makwanni biyu da suka wuce a kasuwar kwanan-gafan babbar kasuwar tumaturin ta Kwanar-gafan kasuwar tunatur ta fadi kasa warwas, inda manoma ke sayar da katon Kwando a kan naira dubu biyu zuwa naira dubu biyu da dari biyar, wannan ta sa yawan masu shanyarsa ya karu. Karuwar masu shanyar ta sa farashin busassahen tumaturin ya fadi kasa warwas.

Duk da cewa, a daidai wannan loacin, lokaci ne na ganiyar samun kaudar tumaturin, kuma yakan yi sauki matuka, wanda har masu sari kan saya su adana shi, to amma a bana faduwar farashin ta yi kasa sosai, saboda wanda yakamata a sayar da shi kuma a yi amfani da shi tun yana danye, yanayi ya sa hakan ba ta yiwu ba.

Manoman tumarurin dai sun koka matuka da faduwar farashin, domin yana taimaka musu wajen samun kudaden yin hidimarsau ta yau da kullum.

Sannan kuma yana taimaka wa manoman wajen yin noman damuna. Saboda haka a bana manoman na tumatur da masu kasuwancin busassahen tumaturin sun shiga halin tsaka-mai-wuya.

Sannan kuma a daidai wannan lokacin da ake sanyi, yawan tumarun da ake diba na karuwa. Ga yawa na karuwa ga farashi na sauka.

Sai dai wani manomi da aka zanta da shi, a kasuwar ta Kwanar-gafan ya tabbatar da cewa, faduwar farashin kaudar tumaturin zai shafi noman damina, domin kudin da suke samu daga noman tumatirin ya ragu kwarai.

Sannan kuma wasu manoman sun bukaci gwamnati da manyan ‘yan kasuwa da su taimaka musu wajen kafa musu masana’antar da za ta sarrafa tumaturin yadda za a iya adana shi, da kuma daukarsa a kai shi sassa daban-daban na ciki da wajen kasar nan. Domin kuwa yin hakan zai taimaka musu wajen rage asarar da suke fuskanta a halin yanzu.

Wani mai kasuwancin kaudar tumaturin da ke zaune a garin Kwanar-dangora, mai suna Sani Bilak, ya koka matuka kan yadda a bana hada-hadar kasuwancin ta su ta samu cikas, wanda ya ce, hakan ta kawo musu cikas matuka.

Don haka, shi ma kiran da nasa ga gwamnati ya yi da manyana ‘yan kasuwa da su samar da hanyar da za a dinga adana tumaturin domin guje wa irin wannan mummunar asara.

Masu shanyar kaudar tumaturin su ma sun ce da gwamnati za ta tallafa musu wajen samar musu da na’urar da za ta busar da tumaturin da an samu saukin yawan asarar da ake yi, sannan kuma zai kasance yana da tsafta, amma a halin yanzu ana sanya shi a wuraen da ba su dace ba. Inda babu cikakkiyar tsafta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarashiTumatir
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara

Next Post

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Related

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

7 days ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

7 days ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 weeks ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Next Post
Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.