ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
Aure

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Mun taba tattauna wannan batu a shafin da muke tattaunawa tare da tsokaci a kan al’amuran zamantakewa na Taskira. Amma saboda muhimmancinsa na ga ya dace na sake dawo da shi a wannan bangare na Marurun Zuciya, saboda wata matsala ce da har yanzu ake fama da ita a cikin al’ummarmu.

Wannan matsala da ke afkuwa ga wasu samarin, bayan kai kudi na gani ina so. Wasu daga cikinsu na daura damarar yin aure, wanda kuma har takan kai da an tura iyaye kai kudin na gani ina so, wanda hakan ke nuni da shaidar an bawa saurayi yarinyar da yake so bisa al’adar Malam Bahaushe.

  • Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma
  • Kotun Ƙoli Ta Sake Tabbatar Da Zaɓen Abiodun A Matsayin Gwamnan Ogun

Wanda kuma hakan ke sa a saka ranar auren masoyan zuwa tsahon wani lokaci. Sai dai wani hanzari ba gudu ba, saka lokaci mai tsaho na aure kan janyo targarda na rugujewar yin auren ga wasu matasan.

Wanda bayan shudewar wasu lokuta da saka rana, iyayen yarinyar kan mayar da kudin auren ba tare da dalilin komai ba. A tawa fahimtar ana samun wannan matsalar ta kowanne bangare, ga su iyayen yarinyar da yarinyar har ma da shi kansa saurayin. Wasu iyayen yarinyar na zaba wa diyarsu namijin da za ta aura ta hangen abin da saurayi yake da shi, musamman wajen ganin yadda yake kashe wa diyarsu kudade masu yawa, yayin da suka samu wanda ya fi shi sai su yanke shawarar mayar wa da yaron kudinsa, musamman in muka yi duba da wannan zamani.

Wasu kuma ba haka bane, bunciken da suka yi ne akan saurayin tun a farko bai yiwu ba, sai bayan lokacin da aka saka ranar aure, sa’annan suke kara samun wasu bayanai a kan yaron, wanda suke ganin yarinyarsu sam! ba ta dace da tsarin yaron ko ahlin yaron ba. Yayin da wasu kuma ke kallon yawan dage-dagen auren da ake yi ke sawa su canja ra’ayinsu gudun kar yarinyarsu ta tsufa a gida. Wasu kuma ganin babu muhallin zama ko kadan ke sawa su fasa bawa yaron ko da kuwa yana da sana’ar yi. Wasu kuma rashin aikin yi da rashin muhalli ke sawa su fasa ba da diyarsu, Wasu kuma umarnin ‘Yarsu kawai suke bi, musamman in ta shiga babbar makaranta sai ta ga sam! ba ajinta ba ne, ko kuma idan ta sami wanda ya fishi sai ta nemi a fasa, su kuma iyayen ba sa duban ka da su zama kananun mutane idan suka maida kudin, amma a haka za su mayar gudun ka da su bata wa diyarsu rai.

Ta bangaren samarin kuwa wasu iyayen saurayin ke sa buri cikin auren wanda har takan kai a rasa lokacin gabatar da auren ko da kuwa an saka ranar auren, akan yawaita daga lokacin auren har ma ya zo ya wuce ba a yi ba, sakamakon burin da aka daukarwa bikin har zuwa lokacin bai gama tabbatuwa ba, har ta kai ga iyayen yarinyar sun gaji da jira sai su fasa. Wani saurayin kuma ya gina soyayyar ne bisa karya, abin da bai da shi ya nuna cewar yana da shi alhalin bai da komai, wani sa’in ma iyayen hayo su yake ba nasa ba ne, komai nasa na aro ne ya ki bayyana kansa a matsayin da yake da shi, wannan ya sa a duk lokacin da gaskiya ta bayyana sai iyayen yarinyar su fasa bawa yaron, domin ko kusa bai dace da diyar su ba.

Wani kuma saurayin yakan boye wasu dabi’unsa ne wanda su kansu iyayensa ba su san yana da dabi’un ba, musamman ta fannin addini ko wasu munanan dabi’un da basu dace da shi ba, a duk lokacin da iyayen yarinya suka gano hakan sukan fasa bawa saurayin diyarsu. Akwai abubuwa da dama wanda ke faruwa har takan ja a mayar da kudin na gani ina so, wanda wajen ya yi kadan a bayyana shi, sai dai a fade su a takaice. Ko shin laifin waye tsakanin Iyayen yarinyar, da yarinyar da shi saurayin? Ko me yake jawo hakan? Ta wacce hanya za a magance matsalar? Za ku iya aiko mana sakonninku ta wannan lamba: 09063836033

Aure
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan'uwansa

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

June 21, 2026
Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

June 21, 2026
Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.