• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
in Marurun Zuciya
0
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye, Saurayi Ko Budurwa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

Mun taba tattauna wannan batu a shafin da muke tattaunawa tare da tsokaci a kan al’amuran zamantakewa na Taskira. Amma saboda muhimmancinsa na ga ya dace na sake dawo da shi a wannan bangare na Marurun Zuciya, saboda wata matsala ce da har yanzu ake fama da ita a cikin al’ummarmu.

Wannan matsala da ke afkuwa ga wasu samarin, bayan kai kudi na gani ina so. Wasu daga cikinsu na daura damarar yin aure, wanda kuma har takan kai da an tura iyaye kai kudin na gani ina so, wanda hakan ke nuni da shaidar an bawa saurayi yarinyar da yake so bisa al’adar Malam Bahaushe.

  • Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma
  • Kotun Ƙoli Ta Sake Tabbatar Da Zaɓen Abiodun A Matsayin Gwamnan Ogun

Wanda kuma hakan ke sa a saka ranar auren masoyan zuwa tsahon wani lokaci. Sai dai wani hanzari ba gudu ba, saka lokaci mai tsaho na aure kan janyo targarda na rugujewar yin auren ga wasu matasan.

Wanda bayan shudewar wasu lokuta da saka rana, iyayen yarinyar kan mayar da kudin auren ba tare da dalilin komai ba. A tawa fahimtar ana samun wannan matsalar ta kowanne bangare, ga su iyayen yarinyar da yarinyar har ma da shi kansa saurayin. Wasu iyayen yarinyar na zaba wa diyarsu namijin da za ta aura ta hangen abin da saurayi yake da shi, musamman wajen ganin yadda yake kashe wa diyarsu kudade masu yawa, yayin da suka samu wanda ya fi shi sai su yanke shawarar mayar wa da yaron kudinsa, musamman in muka yi duba da wannan zamani.

Wasu kuma ba haka bane, bunciken da suka yi ne akan saurayin tun a farko bai yiwu ba, sai bayan lokacin da aka saka ranar aure, sa’annan suke kara samun wasu bayanai a kan yaron, wanda suke ganin yarinyarsu sam! ba ta dace da tsarin yaron ko ahlin yaron ba. Yayin da wasu kuma ke kallon yawan dage-dagen auren da ake yi ke sawa su canja ra’ayinsu gudun kar yarinyarsu ta tsufa a gida. Wasu kuma ganin babu muhallin zama ko kadan ke sawa su fasa bawa yaron ko da kuwa yana da sana’ar yi. Wasu kuma rashin aikin yi da rashin muhalli ke sawa su fasa ba da diyarsu, Wasu kuma umarnin ‘Yarsu kawai suke bi, musamman in ta shiga babbar makaranta sai ta ga sam! ba ajinta ba ne, ko kuma idan ta sami wanda ya fishi sai ta nemi a fasa, su kuma iyayen ba sa duban ka da su zama kananun mutane idan suka maida kudin, amma a haka za su mayar gudun ka da su bata wa diyarsu rai.

Ta bangaren samarin kuwa wasu iyayen saurayin ke sa buri cikin auren wanda har takan kai a rasa lokacin gabatar da auren ko da kuwa an saka ranar auren, akan yawaita daga lokacin auren har ma ya zo ya wuce ba a yi ba, sakamakon burin da aka daukarwa bikin har zuwa lokacin bai gama tabbatuwa ba, har ta kai ga iyayen yarinyar sun gaji da jira sai su fasa. Wani saurayin kuma ya gina soyayyar ne bisa karya, abin da bai da shi ya nuna cewar yana da shi alhalin bai da komai, wani sa’in ma iyayen hayo su yake ba nasa ba ne, komai nasa na aro ne ya ki bayyana kansa a matsayin da yake da shi, wannan ya sa a duk lokacin da gaskiya ta bayyana sai iyayen yarinyar su fasa bawa yaron, domin ko kusa bai dace da diyar su ba.

Wani kuma saurayin yakan boye wasu dabi’unsa ne wanda su kansu iyayensa ba su san yana da dabi’un ba, musamman ta fannin addini ko wasu munanan dabi’un da basu dace da shi ba, a duk lokacin da iyayen yarinya suka gano hakan sukan fasa bawa saurayin diyarsu. Akwai abubuwa da dama wanda ke faruwa har takan ja a mayar da kudin na gani ina so, wanda wajen ya yi kadan a bayyana shi, sai dai a fade su a takaice. Ko shin laifin waye tsakanin Iyayen yarinyar, da yarinyar da shi saurayin? Ko me yake jawo hakan? Ta wacce hanya za a magance matsalar? Za ku iya aiko mana sakonninku ta wannan lamba: 09063836033


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Garkuwa Sun Buƙaci A Biya Su Fansar Miliyan 30 Kan Mutanen Da Suka Sace A Abuja

Next Post

An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

Related

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

5 months ago
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

5 months ago
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

1 year ago
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

1 year ago
Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan
Marurun Zuciya

Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan

1 year ago
Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata
Marurun Zuciya

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

1 year ago
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan'uwansa

LABARAI MASU NASABA

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.