• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

by Leadership Hausa
6 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke, wanda aka fi sani da “Gwamnan Mai Rawa”, ya samu lambar yabo ta LEADERSHIP ta Gwarzon Gwamnan Shekara saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen kawo sauyi da yawa a Jihar Osun.

Jagorancinsa ya ƙunshi inganta ababen more rayuwa da samar da walwalar ma’aikata da tsofaffi da bunƙasa harkokin noma da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa. Wannan karramawa ta nuna yadda jagorancinsa ke inganta rayuwar al’umma cikin gaskiya da aminci.

  • Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

Tarihi da Karatunsa;

An haifi Adeleke a Jihar Osun. Ya fara karatunskaratu a firamare ta Methodist da Nawarudeen, ya yi makarantar sakandare ta Ede Muslim Grammar School Ede, daga nan kuma ya ci gaba da karatunsa a Jami’ar Atlanta Metropolitan State College, inda ya samu digiri a ɓangaren shari’a kan manyan laifuka (Criminal Justice) a 2021. Daga ya ci gaba da ƙara zurfafa iliminsa.

Sanata Adeleke ya fara siyasarsa a 2017, lokacin da ya tsaya takarar Sanatan Osun ta Yamma bayan rasuwar ɗan uwansa, Sanata Isiaka Adetunji Adeleke. Duk da cewa a lokacin yana sabuwar fuska a harkar siyasa amma ya samu nasarar lashe kujerar, duk da kasancewar APC ce mai mulki a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

A 2018, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, inda ya sha gwagwarmayar shari’a kan takararsa. Duk da rasa nasara a kotun ƙoli, ya sake jajircewa da shiryawa don takarar gwamna a 2022, inda ya samu nasarar doke gwamna mai ci, Adegboyega Oyetola. Wannan ya tabbatar da karɓuwarsa a tsakanin jama’ar jihar.

Nasarori A Matsayin Gwamna;

Bayan hawa mulki, Adeleke ya mayar da hankali kan cika alƙawurran da ya ɗaukarwa al’ummarsa yayin yaƙin neman zaɓe. Ya fara kammala ayyukan da aka bari ba a ƙarasa ba, tare da ƙaddamar da sababbin ayyukan da suka shafi rayuwar jama’ar jihar kai-tsaye, kamar hanyoyi da gadaje da gina titunan a faɗin jihar. A cikin watanni 11 na farkon mulkinsa, Adeleke ya fara gadoji a Osogbo da Ile-Ife da Ilesa da kuma Ede. Ya ƙaddamar da tsarin Naira biliyan 100 don ci gabagaba da gudanar da manyan ayyuka ba tare da dogaro da cin bashi ba.

Gwamna Adeleke ya tabbatar da biyan albashi da fansho akan lokaci, yana cika alƙawarinsa na biyan albashin da aka bari bashi a baya. Wannan ya ja hankalin ma’aikatan Jihar Osun, inda suke masa laƙabi da “Mutum na mutane”.

Noma da Kiwo;

Adeleke ya mayar da hankali kan bunƙasa harkokin noma domin inganta samar da abinci da tattalin arziƙin jihar. Ya raba injinan noma da kayan aikin gona ga manoma, ya kuma ƙaddamar da tsarin Osun Broilers Outgrower, wanda ya bayar da tallafi ga masu kiwon Kaji.

A ɓangaren ilimi kuwa, Adeleke ya dawo da tallafin karatu ga ɗalibai a manyan makarantun jihar, ya kuma tabbatar da fara aikin Jami’ar Ilesa da kuma gyaran makarantu a faɗin jihar. Wannan ya ƙara wa yara damar samun ingantaccen ilimi a tsari mai kyau da tsaro.

A ɓangaren lafiya, ya gyara tare da gina sababbin cibiyoyin lafiya sama da 120 daga cikin 345 da ake shirin sabuntawa a jihar. Kazalika, ya gabatar da shirye-shiryen lafiya kyauta, ciki har da tiyatar ido, wanda ake gudanarwa a duk faɗin jihar don tallafa wa jama’a.

Tallafi ga Mata da Matasa

A ƙarƙashin shirin Opon Imo Empowerment, Gwamna Adeleke ya samar da tallafi da horo ga matasa da mata don kafa ƙananan sana’o’i. Wannan ya rage zaman kashe wando tare da ba su damar samun dogaro da kai.

Adeleke ya shahara da halin kula jama’arsa, inda yake sauraron ƙorafe-ƙorafensu tare da mayar da hankali kan ayyukan da za su amfani al’umma. Wannan salon jagoranci ya ƙara masa farin jini da karɓuwa a zuƙatan jama’a, inda ake ganinsa a matsayin jagoran da ke kula da al’ummarsa. Jagorancin Adeleke ya kawo sauyi a Jihar Osun, inda ya tabbatar da cewa kowanne ɓangare na rayuwar al’umarsa sun samu ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #Labarai AdelekeAdelekeAdemola Jackson Nurudeen Adeleke
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bauchi Ta Ba Ma’aikatar Ilimi Muhimmanci A Kasafin Kudin 2025

Next Post

Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

26 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Ademola
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Ademola

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.