ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Jaddada ƙudirin Kare ‘Yancin Faɗin Albarkacin Baki Da ‘Yancin ‘Yan Jarida

by Sulaiman
1 year ago
Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada ƙudirin ta na kare ‘yancin faɗin albarkacin baki, ƙarfafa adawa mai amfani, da samar da yanayi mai kyau ga ‘yan jarida a Nijeriya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da ake ci gaba da Zauren Bayani na Ministoci da ake gudanarwa a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina

Ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jajircewa wajen kare ‘yanci da kundin tsarin mulki ya tanada, tare da ƙarfafa mahawara mai amfani domin inganta dimokiraɗiyya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

Ya ce: “Ina so in sake nanata cewa Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda yake cikakken ɗan dimokiraɗiyya, yana da niyyar kare ‘yancin ‘yan Nijeriya kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada. Haka zalika, yana ƙarfafa sukar gwamnati mai ma’ana da adawa tagari saboda suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen ingantawa da zurfafa tsarin dimokiraɗiyyar mu.

 

“Ina kuma tabbatar da cewa wannan gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin ‘yan jarida da samar da yanayi mai kyau ga aikin jarida a Nijeriya. Gwamnatin nan tana da yaƙinin cewa ‘yancin ‘yan jarida yana da muhimmanci wajen inganta nagartar shugabanci, gaskiya, da ci gaban ƙasa.”

 

Ministan ya yi amfani da damar taron don taya Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) murnar cika shekaru 70, yana mai bayyana wannan lokaci a matsayin wata babbar alama ta jajircewar su wajen kare ‘yancin ‘yan jarida da inganta aikin jarida.

 

Ya ce: “Ina kuma so in gode wa kafafen yaɗa labarai saboda jajircewar su wajen yaɗa muhimman batutuwan gwamnati. Wannan taro yana gudana a cikin wani lokaci mai muhimmanci, yayin da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) take bikin cika shekaru 70. Wannan babbar alama ce da ke nuna yadda NUJ ke ci gaba da jajircewa kan ‘yancin ‘yan jarida da ingancin aikin jarida.”

 

Idris ya bayyana cewa Zauren Taron Bayani na Ministoci da ma’aikatar sa take jagoranta yana da manufar bai wa ‘yan Nijeriya damar samun cikakken bayani kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na nuna gaskiya da ɗaukar alhakin ayyukan ta.

 

“Wannan taro wata babbar dama ce ga ministoci su sanar da ‘yan Nijeriya irin cigaban da aka samu a ma’aikatun su. Ta wannan zauren tattaunawar, wanda aka inganta ta hanyar fasahohin zamani, muna tabbatar da ƙudirin mu na bayyana gaskiya da bayar da bayanai kai-tsaye dangane da manufofi, shirye-shirye, da sauye-sauyen da ke faruwa a ma’aikatun gwamnati.”

 

Ministan ya yaba wa Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, bisa ƙoƙarin sa na inganta martabar Nijeriya a idon duniya ta hanyar manufofin diflomasiyya da tsare-tsaren hulɗa da ƙasashen ƙetare.

 

Haka nan, ya jinjina wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, saboda irin sauye-sauyen da yake aiwatarwa domin daidaita ma’aikatar daidai da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Tinubu.

Gwamnati
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
  • Sulaiman
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • Sulaiman
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Next Post
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

July 5, 2026
Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

July 5, 2026
Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.