Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Gwamnatin Nijeriya Ta Fitar Da Sabon Tsarin Canja Layin Waya

by Yusuf Shuaibu
January 4, 2021
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Tsarin Canja Layin Waya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnatin tarayya ta fitar da sabon tsari wajen canza layin wayar salula ga  kamfanonin sadarwa a Nijeriya. Ta bayyana cewa, ta fitar da wannan sabon tsarin ne domin tabbatar da ganin an hade kowani da yi da katin lambar dan kasa. Ta kara da cewa, za ta yi aiki kafada da kafada da dukkanin masu ruwa da tsaki da ke cikin kamfanonin sadarwa wajen tabbatar da ganin an yi aiki da wannan sabon tsarin.

Sabon tsari a kan canza layin wanda ministan sadarwa da tattalin arzikin kimiyya, Isa Pantami ya amince da shi, an samar da shi ne ga wadanda layukansu ya bace ko ya lalace ko aka sace.

samndaads

Gwamnatin tarayya da bayyana wannan ne a wani takarda da jami’in hudda da jama’a na hukumar sadarwa, Ikechukwu Adinde da babban jami’in sadarwa a hukumar kula da katin dan kasa, Kayode Adegoke suka rattaba hannu. gwamanatin tarayya ta bayayana cewa, yanayin yadda za a dunga canza layukan dai shi ne, dole ne sai wanda zai canza layi ya nuna lambar katin zama dankasa kafin a canza masa layi. Wannan yana daga cikin ka’idojin hukumar sadarwa ta kasa ta gindaya na saka sabon layi.

A ranar 15 ga watan Disambar shekarar 2020, gwamnatin tarayya ta sanar da cewa dole ne kowani layin waya a hade shi da katin lambar dan kasa kafin ranar 30 ga watan Disambar shekarar 2020, inda ta umurci kamfanonin sadarwa su rufe duk wani layin waya da ba a hade da lambar dan kasa ba idan wa’adin ya wuce. Amma daga baya an kara tsawan makwanni uku sakamakon an gudanar da sanarwar da wuri, inda aka ka ihi zuwa ranar 19 ga watan Junairun shekarar 2021. Daga baya kuma an kara wa’adin mako shida wanda ya sa aka kai shi zuwa ranar 9 ga watan Fabrairun shekarar 2021.

“Kwamitin zai saka ido ne wajen tabbar da an hade layukan waya da lambar katin dan kasa .”

Ta kara da cewa, bisa amincewar wannan kwamiti ne ya bayar da damar aiwatar da wannan sabon tsari a kan canza layin wayar salula. Ta ce, an aiwatar da tsarin ne domin ya bai wa kamfanonin sadarwa gane wanda ke bukatar canza layin waya, ga mutanen da layin su ya lalace ko aka sace ko ya bace, wanda cikin sauki kamfanonin sadarwar za su canza layin.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

An Nuna Bukatar Kawo Karshen Talauci A 2021 A Nijeriya

Next Post

An Jinjina Wa Mambobin WUCOBA 86 Bisa Halartar Taron Kungiyar

RelatedPosts

FIRS

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

by Yusuf Shuaibu
11 hours ago
0

Hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS) ta bayyana cewa, ta...

Samar Da Allurar Rigakafin COVID-19 Cikin Adalci Zai Taimaka Wa Afirka Wajen Yakar Annobar

Gwamnatin Nijeriya Ta Ware Naira Biliyan 10 Domin Samar Da Magungunan Korona

by Yusuf Shuaibu
11 hours ago
0

Ma’aikatar kudi ta ware naira biliyan 10 domin samar da...

cbn

CBN Ta Bada Tallafin Biliyan N10 Domin Farfado Da Kamfanoni A Kano

by Yusuf Shuaibu
11 hours ago
0

Kungiyar zuba jari ta Jihar Kano tare da hadin gwiwar...

Next Post
WUCOBA

An Jinjina Wa Mambobin WUCOBA 86 Bisa Halartar Taron Kungiyar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version