• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Rufe Iyakokin Nijeriya Da Nijar

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Rufe Iyakokin Nijeriya Da Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta ba da umarnin rufe dukkan iyakokin kasar da Jamhuriyar Nijar cikin gaggawa saboda tabarbarewar siyasar da ake fama da ita a kasar.

Manufar umarnin a cewar Mukaddashin Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi Adewale, za ta amfanar kasashen biyu.

  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara
  • Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

Adewale, wanda ya kasance a kan iyakar Jibia a jihar Katsina, domin sanya ido kan matakin da ake bi, ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta umarci masu ruwa da tsaki a harkokin kan iyakokin da su tabbatar da bin ka’idar umarnin.

“Kamar yadda muka sani, shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu dan gwagwarmaya ne na hadakar tattalin arziki a yammacin Afirka. Ya yi imanin cewa kasuwanci da makwabciyarmu zai iya kawo ci gaba ga ‘yan Nijeriya da sauran jama’ar yankin,” in ji shi.

“Watakila wannan mataki ya taimaka masa wajen samun nasararsa a matsayin shugaban ECOWAS cikin wata guda da hawansa shugabancin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

“Yanzu, muna da wani yanayi a hannunmu inda ake fama da rashin zaman lafiya da rashin tsaro. Wannan yanayin ba zai ba da damar bunkasar ciniki ba. Ba za mu iya samun kasuwanci mai ma’ana ba a cikin yanayi na rashin tsaro da rashin zaman lafiya da ke faruwa a Jamhuriyar Nijar.

“Don haka ne kungiyar ECOWAS, ta hannun ikon shugabanta, ta dauki matakin rufe dukkan iyakokin kasa da Jamhuriyar Nijar.”

A cewarsa, hukumar ta tura jami’ai kan iyakokin Nijeriya da Nijar don tabbatar da tsaro.

“Hakki ne da ya rataya a wuyan hukumar Kwastam ta Nijeriya, tare da yin aiki tare da sauran hukumomin gwamnati, don aiwatar da abin da ya dace.

“Hukumar kwastam ta Nijeriya ta yi hadin gwiwa da sauran jami’an tsaro a kan iyaka domin aiwatar da dokar rufe iyakokin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASJuyin MulkiNijarNijeriyaRufe IyakokiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mai Magana Da Yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Yi Karin Haske Kan Bayanan Kafofin Watsa Labarai Game Da Sanarwar Italiya Na Kin Tsawaita Yarjejeniyar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Next Post

Abubuwan Da Suka Gudana A Zanga-zangar Cire Tallafin Mai

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

21 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

22 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Abubuwan Da Suka Gudana A Zanga-zangar Cire Tallafin Mai

Abubuwan Da Suka Gudana A Zanga-zangar Cire Tallafin Mai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.