• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar

by Sadiq
3 years ago
Zamfara

Gwamna Bello Matawalle, ya ce gwamnatin Jihar Zamfara ta gano akalla likitocin bogi 199 da ke cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan gwamnatin jihar.

Matawalle ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Maradun, hedikwatar karamar hukumar Maradun ta jihar.

  • Mutum Daya Ya Mutu A Rikicin Fulani Da Patigi A Kwara 
  • Zargin Sace 89trn: Dan Takara A Kano Zai Maka Buhari A Kotu

A cewar gwamnan, duk da cewa gwamnatin jihar na biyan albashi ga likitoci 280 duk wata, amma ta gano likitoci 81 ne kawai ke aiki a fadin jihar.

Ya kuma bayyana cewa tuni ya gana da kungiyar kwadago ta NLC reshen jihar kan yadda za a gano wadancan likitocin bogi 199 da suka dauki tsawon lokaci suna karbar albashi ba bisa ka’ida ba.

Matawalle ya bayyana cewa, gano likitocin bogin ya biyo bayan ci gaba da binciken bayanan da ake yi wa daukacin ma’aikatan jihar ta ofishin shugaban ma’aikatan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

An ce aikin tattara bayanan na nuni ne da shirin gwamnatin jihar na fara aiwatar da tsarin mafi karancin albashi na Naira 30,000 ga ma’aikatan jihar.

“Matsalar ita ce, da zarar mun ce za mu aiwatar da shi (N30,000), ba za mu iya cewa za mu biya mutane kai tsaye haka ba. A’a, akwai tsari,” in ji Matawalle.

“Mun samar da tsari, kuma abin takaici, a lokacin aiki, an gano cewa akwai likitoci sama da 280 da suke karbar albashi daga gwamnatin jihar nan, amma a gaskiya muna da likitoci 81 ne kawai na gaskiya a Jihar Zamfara.

“Kungiyar kwadago ta tabbatar min dalilin da ya sa suka jinkirta shirin – cewa suna son tabbatar da cewa abubuwa sun tafi daidai saboda ba za mu iya ci gaba da hakan a matsayin gwamnati ba.”

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa babu wani ma’aikaci na gaskiya da gwamnatinsa za ta yi murabus dangane da aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000.

“Ba zan sake mayar da kowa ba. A gaskiya zan ba su gidajen (ma’aikatan gwamnati) na duk ma’aikatan gwamnati. Na gina musu gidaje 450 wadanda babu wanda ya san su, amma ranar Lahadi zan ba su makullin,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
Manyan Labarai

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
Manyan Labarai

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Next Post
Gobara Ta Kone Hedikwatar ‘Yansanda A Kano

Gobara Ta Kone Hedikwatar 'Yansanda A Kano

LABARAI MASU NASABA

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.