• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Bello Matawalle, ya ce gwamnatin Jihar Zamfara ta gano akalla likitocin bogi 199 da ke cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan gwamnatin jihar.

Matawalle ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Maradun, hedikwatar karamar hukumar Maradun ta jihar.

  • Mutum Daya Ya Mutu A Rikicin Fulani Da Patigi A Kwara 
  • Zargin Sace 89trn: Dan Takara A Kano Zai Maka Buhari A Kotu

A cewar gwamnan, duk da cewa gwamnatin jihar na biyan albashi ga likitoci 280 duk wata, amma ta gano likitoci 81 ne kawai ke aiki a fadin jihar.

Ya kuma bayyana cewa tuni ya gana da kungiyar kwadago ta NLC reshen jihar kan yadda za a gano wadancan likitocin bogi 199 da suka dauki tsawon lokaci suna karbar albashi ba bisa ka’ida ba.

Matawalle ya bayyana cewa, gano likitocin bogin ya biyo bayan ci gaba da binciken bayanan da ake yi wa daukacin ma’aikatan jihar ta ofishin shugaban ma’aikatan jihar.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

An ce aikin tattara bayanan na nuni ne da shirin gwamnatin jihar na fara aiwatar da tsarin mafi karancin albashi na Naira 30,000 ga ma’aikatan jihar.

“Matsalar ita ce, da zarar mun ce za mu aiwatar da shi (N30,000), ba za mu iya cewa za mu biya mutane kai tsaye haka ba. A’a, akwai tsari,” in ji Matawalle.

“Mun samar da tsari, kuma abin takaici, a lokacin aiki, an gano cewa akwai likitoci sama da 280 da suke karbar albashi daga gwamnatin jihar nan, amma a gaskiya muna da likitoci 81 ne kawai na gaskiya a Jihar Zamfara.

“Kungiyar kwadago ta tabbatar min dalilin da ya sa suka jinkirta shirin – cewa suna son tabbatar da cewa abubuwa sun tafi daidai saboda ba za mu iya ci gaba da hakan a matsayin gwamnati ba.”

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa babu wani ma’aikaci na gaskiya da gwamnatinsa za ta yi murabus dangane da aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000.

“Ba zan sake mayar da kowa ba. A gaskiya zan ba su gidajen (ma’aikatan gwamnati) na duk ma’aikatan gwamnati. Na gina musu gidaje 450 wadanda babu wanda ya san su, amma ranar Lahadi zan ba su makullin,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Likitocin BogiMatawalleZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum Daya Ya Mutu A Rikicin Fulani Da Patigi A Kwara 

Next Post

Gobara Ta Kone Hedikwatar ‘Yansanda A Kano

Related

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

9 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

11 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

15 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

16 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

21 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 day ago
Next Post
Gobara Ta Kone Hedikwatar ‘Yansanda A Kano

Gobara Ta Kone Hedikwatar 'Yansanda A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.