• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Afirka

Karshen shekara lokaci ne na waiwaye adon tafiya. Sai dai a wannan shekarar da muke ciki, mun gane ma idanunmu dimbin abubuwan takaici da suka abku a duniya. Wani abu da zai iya sanyaya zuciyarmu shi ne, yadda huldar hadin gwiwa ta Sin da Afirka ke bunkasa yadda ake bukata. Kamar dai yadda shugaba Bola Tinubu na kasar Najeriya ya fada, a taron kolin dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a bana, cewa ”yayin da ake fuskantar kalubalolin tattalin arziki da na siyasa dake addabar duniya, huldar Afirka da Sin ta nuna yanayi na jajircewa, ta yadda ta zama wani abin koyi ga kasa da kasa.”

 

Dangane da jajircewar da shugaba Tinubu ya ambata, za a samu cikakken bayani ne cikin jawabin da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi a jiya Talata, kan ayyukan da aka yi a kasar Sin a fannin diplomasiyya cikin shekarar 2024. A cikin jawabin, Wang ya ambaci sakamakon taron koli na dandalin FOCAC da ya gudana a Beijing a wannan karo, yana cewa, ”Shugabannin Sin da Afirka sun cimma ra’ayi daya, kan gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya ta sabon zamani, dake iya jure duk wani yanayi.” To, maganar ”jure duk wani yanayi” da ”jajircewa” suna da ma’ana kusan iri daya. Wato duk wani kalubale da ake fuskanta, kuma duk wata matsalar da ake fama da ita, Sin da Afirka za su yi kokarin neman ci gaba na bai daya, kafada da kafada.

  • Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya
  • Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

To, sai dai ta yaya ake aiwatar da matsayar da aka cimma? Wang ya ambaci wasu matakan tallafawa kokarin raya kasa guda 8, da Sin take gudanar da su a hadin gwiwarta da dimbin kasashen dake nahiyar Afirka, wadanda suka shafi rage talauci, da samar da isasshen abincin da ake bukata, da kirkiro sabbin fasahohi, da dai sauransu. Kana jami’in ya ambaci yadda kasar Sin ta cire kudin kwastan kan kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, da aikin hadin kai da Sin da Afirka ke gudanarwa, mai nasaba da fannoni 10 da suka hada da ciniki da zuba jari, da tsarin samar da kayayyaki, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

Sai dai don tabbatar da jajircewar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ban da ingantattun manufofin da ake aiwatar da su a halin yanzu, ana bukatar samun hasashe mai yakini kan makomar huldar. Dangane da wannan fanni, za mu iya duba jawaban da aka yi wajen muhawarar Mjadala Afrika, da ta gudana a kasar Habasha a kwanakin nan. An yi muhawarar ne tsakanin mutane masu takarar neman kujerar shugaban majalissar kungiyar kasashen Afirka ta AU, inda aka ba mutanen da za su iya zama shugaban majalissar kungiyar AU damar bayyana manufofin raya nahiyar Afirka da za su iya dauka a nan gaba, idan sun ci nasarar lashe zaben.

 

Sai dai a bisa ra’ayin ‘yan takara na kasashen Kenya, da Djibouti, da Madagascar, da dai sauransu, makoma mai haske ta nahiyar Afirka ta dogara kan karfafa huldar abota, da za ta tabbatar da kirkire-kirkire, da adalci, da samun ci gaba tare, inda kasar Sin za ta taka rawar gani a ciki.

 

Abun lura shi ne, burikan da wadannan ‘yan siyasa suka ambata a jawabansu, irinsu kokarin gina yankin ciniki cikin ‘yanci na Afirka, da karfafa ciniki tsakanin kasashen Afirka, da amfani da tsarin fasahar dijital wajen sa ido kan yadda ake aiwatar da Ajandar 2063, da inganta kwarewar kasashen Afirka a fannonin tinkarar bazuwar annoba da ke abkuwa ba zato ba tsammani, da nemo kayayyakin aikin jinya da ake bukata, sun dace da matakan hadin gwiwar da ake yi tsakanin Sin da Afirka, da ta shafi aiwatar da shawarar ”Ziri Daya da Hanya Daya”, da yada fasahohin dijital zuwa karin wurare, da aikin jinya, da dai makamantansu. To, wadannan abubuwa sun shaida cewa, akwai tabbaci ga huldar hadin kai ta Sin da Afirka, cikin wani dogon lokaci mai zuwa.

 

Cikin jawabinsa ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kasar Sin za ta yi amfani da yanayin tabbas da take da shi wajen tinkarar yanayin rashin tabbaci da ake fama da shi a duniya. To, a ganina, jajircewar huldar hadin kai tsakani Sin da Afirka ita ma tana samar da tabbaci, da imani, da kwanciyar hankali ga duniyarmu, da ke fama da yanayin tangal-tangal a halin da muke ciki. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Afirka
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Next Post
Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.