• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa halin ‘yan siyasa na bai wa sarakuna mamaki.

Mamakin da suke yi wa ‘yan siyasa, a cewarsa shi ne, lokacin da ‘yan siyasa ke yakin nema zabe sai su zo wurinsu, amma da zarar sun samu nasara ba a kara jin duriyarsu sai bayan shekaru hudu. Ya kara da cewa sarakuna na bukatar samun matsayi a tsarin mulki ba wai saboda yukurin kirkiro wani bangare na gwamnati ba ne a cikin kasar nan.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kafanchan

Sarkin Zazzau ya bayyana hakan ne a lokacin da shugaban majalisar wakilai, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya ziyarce shi a fadarsa da ke Zariya ta Jihar Kaduna.

“Ba za a iya bata kwatanta irin gudummuwar da sarakuna suke bayarwa ba, saboda sarakuna suna taka muhimmiyar rawa tun fara mulkin dimokuradiyya har zuwa yau. Na san cewa mafi yawancinku a nan kuna da alaka da sakakuna ko ta kusa ko ta nesa.

“Abin da yake ba mu mamaki shi ne, mutane suna zuwa wurinmu neman tabarraki lokacin zabe, amma da zarar sun samu nasara, ba za su sake dawowa ba sai lokacin zabe kana su kara tuntubarmu. Kafin yanzu, muna mamakin yadda ake yi wa sarakuna haka, amma kuma sun kasa ganewa cewa su sarakuna a ko da yaushe suna nan kan mukaminsu, ko muna raye ko mun mutu. Duk inda mutum ya je sai ya dawo wurinmu.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

“Muna jin yadda wasu ‘yan siyasa ke cewa muna son kirkiro wani bangare na gwamnati. Ina magana amadadin sauran sarakuna kamar irinsu Mai Alfarma Sarkin Musulmi da Shehun Borno da sauran sarakuna. Mun tattauna kan wannan matsala babu adadi.

Mun je Abuja, inda muka gana da tsohon shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai. Mun gabatar da matsayinmu karkashin jagorancin Sarkin Lafiya wanda shi tsohon alkalin kotun koli ne. Mun zayyana matsayinmu, inda muka mika wa tsohon shugaban majalisar dattawa, mun yi mamakin yadda aka yi watsi da kudurin namu.

“Ina magana ne amadadin daukacin sarakunan Arewa. Muna fatan majalisar kasa da duba wannan kurin tare da aiki a kansa da kuma tabbatar ya zama doka.”
Ya kara da cewa babu abin da Masarautar Zazzau za ta iya cewa sai dai godiya ga Allah da ya azurtata.

Ya ce masarautar da kyankyashe shahararrun ‘yan Nijeriya tun daga kan tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon da tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo da ministoci da dama da sakatarorin gwamnatin tarayya, yanzu kuma ga shugaban majalisar wakilai.

Da yake jawabi, Rt. Hon Tajudeen Abbas ya sha alwashin cewa majalisa ta 10 za ta karkiri matsayin sarakuna a cikin kundin tsarin mulkin kasar nan.

Shugaban majalisar wakilai wanda shi dan asalin garin Zariya ne da yake wakiltar mazabar Zariya a zauren majalisa kuma yana da sarauta a cikin masarautar. Ya ce shi da kansa da kuma sauran ‘yan majalisan wakilai sun fahimci muhimmancin sarakuma, sannan za su tabbatar da cewa sun saka su a cikin kundin tsarin mulki.

“Tun shekaru uku da suka gabata na san cewa akwai takardar da majalisar sarakunan kasar nan suka gabatar, inda suka bayyana yadda sarakuna ya kamata su yi aiki a wannan zamani. Muna yi wa Allah godiya da ya kaddara danku ya zama shugaban majalisar wakilai kuma zai sake yin nazari kan matsayin sarakuna.

“Ina mai tabbatar muka cewa ni da suran ‘yan majalisa za mu sake bankado takardar da majalisar sarakuna ta rubuta domin tabbatar da cewa an sama aikin sarakuna a cikin kundin tsarinmulki.

“Za mu yi aiki kafada da kafada da dukkan majalisun kasa domin sake dawo da martabar sarakunan gargajiya.”
Ya nuna jin dadinsa ga sarkin da kuma daukacin mutanen masarautar Zazzau bisa wannan ziyara ta farko tun bayan da ya zama shugaban majalisar wakilai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Daliban Jami’a 3 Kan Kashe Direban Mota

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Siyasa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

'Yansanda Sun Cafke Daliban Jami'a 3 Kan Kashe Direban Mota

LABARAI MASU NASABA

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.