• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar

byLeadership Hausa
2 years ago
Nijar

Nijeriya da Nijar ‘yan’uwan juna ne, ana kuma sa ran za su ci gaba da kasancewa a matsayin ‘yan’uwan junan. Don haka, ka da mu yarda mu rudu da jin cewa muna da karfi ko kwarewa da za ta sa mu afka wa juna ta fuska yaki, musamman idan muka yi la’akari da abin da ya faru da Kasar Ukraine, ya isa mu gane cewa ba a taba yin bari a kwashe duka.

Shugabanci ya kunshi abubuwa da dama da suka hada da samar da masalaha, tuntuba da kuma ba da damar tattaunawa domin samar da maslaha a tsanin bangarori daban-daban. Don haka, idan har muna bukatar ci gaba da zama a matsayin ‘yan’uwan juna, wajibi ne mu ci gaba da aiwatar da harkokinmu a matsayin ‘yan Afrika kuma uwa daya uba daya. kazalika, dole ne mu fahimci yadda za rika zama muna tattaunawa a tsakanin duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar

Haka zalika, ya kyautu a rika baiwa kowa ‘yancin da yake da shi tare da samar da kyakkyawar hanyar tattaunawa a lokacin da ya dace, musamman idan akwai bukatar hakan, ko da kuwa abin da ya shafi kungiyar ECOWAS ne, wannan dalili ne ma ya sa kasashen Afrikan suka shiga wannan kungiya, har ake zaben shugabanni lokaci zuwa lokaci, wanda hakan yasa aka zama kamar uwa daya uba daya.

Bugu da kari, ya zama tilas mu koyi yadda za mu rika warware matsalolinmu a tsakanin mu na mutanen Afrika, duk wani kutse da turawan yamma za su yi a tsakanin mu da sunan taimako, babu abin da zai tsinana mana illa sake jefa mu halin ha’u’la’i. Idan muka yi la’akari da magabatan shugabanninmu na Afrika irin su marigayi Tafawa Balewa, Kwame Nkrumah Julius Nyerere, Milton Obote, Samora Mitchel, Banda, Omar Bongo, Ahamadou Ahidjo, Senghore, Mandela da sauran makamantansu, sun hada kan Afrika tamkar uwa daya uba daya.

Saboda haka, babu yadda za a yi a halin yanzu mu zauna kanmu a rarrabe sannan mu yi tsammanin samun ci gaba ko hadin kai a wadannan yankunan namu na Afrika ba. Don haka, ya kyautu kungiyar ECOWAS ta yi hobasa wajen wanzar da zaman lafiya, hadin kai da kuma kawo ci gaba ga yankunan Afrika tare da sasanta tsakanin ‘ya’yayen nata a matsayinsu na bakar fata, ba wai kasashe irin su Birtaniya, Faransa, Fotigal ko kuma kasashen Larabawa ba, a’a kawai ya kasance Afrika ita ce farko aiwatar da hakan.

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Sojojin da suka yi juyin mulki a Kasar Nijar, kamar abin da ya faru ne a sauran kasashe kamar irin su; Mali, Guinea, Burkina Faso da sauran makamantansu, wanda hakan na nuna baro-baro cewa akwai alamun zalinci tare da cin amanar wadanda suka zabe su, ta hanyar rashin cika alkawarurrukan da suka yi musu, ga kuma uwa-uba bakin talaucin da suke fama da shi sakamakon rikon sakainar kashin da shugabannin nasu suka yi musu. Saboda haka, ya kyautu shugabanni su koyi magana da harshe daya, idan suka fada su rika cikawa.

A halin da ake ciki yanzu, kusan duniya baki-daya na fama da masifu iri daban daban da ya hada da matsalar zaizayar kasa, ambaliyar ruwa, yake-yake da sauran makamantansu. Wadannan dalilai kadai sun isa su sa kungiyar ECOWAS ta shiga hankalinta da kuma sauya tunani. Kasar Nijar babbar garkuwa ce ta fuskar tsaro idan aka yi la’akari da Sahara da take da shi, far mata kan haifarwa kungiyar ECOWAS da mara ido, ta hanyar rikice-rikice tare da bude kofar shigo da makamai wanda hakan kan yi sanadiyar hallaka mu baki-daya.

Don haka, muna kira da babbar murya ga kungiyar ECOWAS, da ta dubi Allah ta samar da hanyoyin warware wadannan matsalolin cikin ruwan sanyi, ba tare da amfani da karfin Soja ba.

Abraham James, Kwararre

ne a kan sadarwa da harkokin Difilomasiyya da ke Nijeriya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version