• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar

by Leadership Hausa
2 years ago
in Ra'ayoyi
0
Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya da Nijar ‘yan’uwan juna ne, ana kuma sa ran za su ci gaba da kasancewa a matsayin ‘yan’uwan junan. Don haka, ka da mu yarda mu rudu da jin cewa muna da karfi ko kwarewa da za ta sa mu afka wa juna ta fuska yaki, musamman idan muka yi la’akari da abin da ya faru da Kasar Ukraine, ya isa mu gane cewa ba a taba yin bari a kwashe duka.

Shugabanci ya kunshi abubuwa da dama da suka hada da samar da masalaha, tuntuba da kuma ba da damar tattaunawa domin samar da maslaha a tsanin bangarori daban-daban. Don haka, idan har muna bukatar ci gaba da zama a matsayin ‘yan’uwan juna, wajibi ne mu ci gaba da aiwatar da harkokinmu a matsayin ‘yan Afrika kuma uwa daya uba daya. kazalika, dole ne mu fahimci yadda za rika zama muna tattaunawa a tsakanin duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar

Haka zalika, ya kyautu a rika baiwa kowa ‘yancin da yake da shi tare da samar da kyakkyawar hanyar tattaunawa a lokacin da ya dace, musamman idan akwai bukatar hakan, ko da kuwa abin da ya shafi kungiyar ECOWAS ne, wannan dalili ne ma ya sa kasashen Afrikan suka shiga wannan kungiya, har ake zaben shugabanni lokaci zuwa lokaci, wanda hakan yasa aka zama kamar uwa daya uba daya.

Bugu da kari, ya zama tilas mu koyi yadda za mu rika warware matsalolinmu a tsakanin mu na mutanen Afrika, duk wani kutse da turawan yamma za su yi a tsakanin mu da sunan taimako, babu abin da zai tsinana mana illa sake jefa mu halin ha’u’la’i. Idan muka yi la’akari da magabatan shugabanninmu na Afrika irin su marigayi Tafawa Balewa, Kwame Nkrumah Julius Nyerere, Milton Obote, Samora Mitchel, Banda, Omar Bongo, Ahamadou Ahidjo, Senghore, Mandela da sauran makamantansu, sun hada kan Afrika tamkar uwa daya uba daya.

Saboda haka, babu yadda za a yi a halin yanzu mu zauna kanmu a rarrabe sannan mu yi tsammanin samun ci gaba ko hadin kai a wadannan yankunan namu na Afrika ba. Don haka, ya kyautu kungiyar ECOWAS ta yi hobasa wajen wanzar da zaman lafiya, hadin kai da kuma kawo ci gaba ga yankunan Afrika tare da sasanta tsakanin ‘ya’yayen nata a matsayinsu na bakar fata, ba wai kasashe irin su Birtaniya, Faransa, Fotigal ko kuma kasashen Larabawa ba, a’a kawai ya kasance Afrika ita ce farko aiwatar da hakan.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Sojojin da suka yi juyin mulki a Kasar Nijar, kamar abin da ya faru ne a sauran kasashe kamar irin su; Mali, Guinea, Burkina Faso da sauran makamantansu, wanda hakan na nuna baro-baro cewa akwai alamun zalinci tare da cin amanar wadanda suka zabe su, ta hanyar rashin cika alkawarurrukan da suka yi musu, ga kuma uwa-uba bakin talaucin da suke fama da shi sakamakon rikon sakainar kashin da shugabannin nasu suka yi musu. Saboda haka, ya kyautu shugabanni su koyi magana da harshe daya, idan suka fada su rika cikawa.

A halin da ake ciki yanzu, kusan duniya baki-daya na fama da masifu iri daban daban da ya hada da matsalar zaizayar kasa, ambaliyar ruwa, yake-yake da sauran makamantansu. Wadannan dalilai kadai sun isa su sa kungiyar ECOWAS ta shiga hankalinta da kuma sauya tunani. Kasar Nijar babbar garkuwa ce ta fuskar tsaro idan aka yi la’akari da Sahara da take da shi, far mata kan haifarwa kungiyar ECOWAS da mara ido, ta hanyar rikice-rikice tare da bude kofar shigo da makamai wanda hakan kan yi sanadiyar hallaka mu baki-daya.

Don haka, muna kira da babbar murya ga kungiyar ECOWAS, da ta dubi Allah ta samar da hanyoyin warware wadannan matsalolin cikin ruwan sanyi, ba tare da amfani da karfin Soja ba.

Abraham James, Kwararre

ne a kan sadarwa da harkokin Difilomasiyya da ke Nijeriya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Halin Da Masu Kananan Sana’o’i Ke Ciki (3)

Next Post

Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

3 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

8 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

9 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

9 months ago
BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

9 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

10 months ago
Next Post
Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

Aliyev: Azerbaijan Na Kokarin Yin Hadin Gwiwa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.