• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

Ana Yi Wa 'Yan F im Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi'u Ali

by Rabilu Sanusi Bena
5 months ago
Hukuma

A ƙoƙarinta na tabbatar ta bin dokar tace fina-finai sau da ƙafa tare da ƙara ɗora masana’antar Kannywood a kan saiti, hukumar tace fina-finai da Ɗab’i ta Jahar Kano ƙarƙashin jagorancin Alh Abba El-mustapha ta ɗauki wani mataki domin tsaftace yadda ake sakin fina-finai barkatai ba tare da cika ƙa’idar da doka ta tanadar musu ba, na kawo kowanne Fim gabanta a tantance shi kafin ya isa ga idanun al’umma inda ta dakatar da cigaba da haska wasu Manyan Fina-finai har guda 22.

Abba El-mustapha ne ya bayyana wannan mataki biyo bayan tattaunawa da manyan jami’an hukumar tare da dogon nazari domin kawo ƙarshen ƙorafe-ƙorafen da yace hukumar ke yawan karɓa don ƙara inganta aiyukan hukumar tare da masana’antar Kannywood, sanarwar tace hukumar ba zata lamunci karan tsaye akan harkar Fim ba a jihar Kano ba.

  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Ya ƙara da cewa doka ce ta bawa hukumar damar tace duk wani Fim tare da lura da aiyukan yan masana’antar Kannywood matsawar suna da rijista da hukumar a ko ina suke, saboda haka ana shawartar masu ɗaukar nauyin waɗannan fina-finai da su tabbatar da sun bi wannan doka ta dakatarwa tare da tsayar da saka waɗannan fina-finai a gidajen TV ko kafar intanet.

Haka kuma ana sanar da su cewa su miƙo fina-finansu ga hukumar domin tantance su tare da ba su shaidar inganci ta tacewa nan da sati ɗaya mai zuwa domin guje wa fushin doka.

Daga ƙarshe hukumar ta nemi haɗin kan dukkannin gidajen TV da hukumar da ke lura da kafafen yaɗa labarai ta Nijeriya wato NBC kan su cigaba da taimaka mata wajen samun nasarar abinda ta saka a gaba da cigaban Jihar Kano da masana’antar Kannywood.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

jami’in yaɗa labaran hukumar Abdullahi Sani Suleiman ya bayyana fina-finan da aka dakatar kamar haka:

1. Dakin Amarya  

2. Mashahuri  

3. Gidan Sarauta  

4. Wasiyya  

5. Tawakkaltu  

6. Mijina  

7. Wani Zamani  

8. Labarina  

9. Mallaka  

10. Kudin Ruwa  

11. Boka Ko Malam  

12. Wa yasan Gobe  

13. Rana Dubu  

14. Manyan Mata  

15. Fatake  

16. Gwarwashi  

17. Jamilun Jiddan  

18. Shahadar Nabila  

19. Dadin Kowa  

20. Tabarma

21. Kishiyata

22. Rigar Aro

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Next Post
Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri

Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Hukuma

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.