• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

Ana Yi Wa 'Yan F im Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi'u Ali

by Rabilu Sanusi Bena
5 months ago
in Nishadi
0
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarinta na tabbatar ta bin dokar tace fina-finai sau da ƙafa tare da ƙara ɗora masana’antar Kannywood a kan saiti, hukumar tace fina-finai da Ɗab’i ta Jahar Kano ƙarƙashin jagorancin Alh Abba El-mustapha ta ɗauki wani mataki domin tsaftace yadda ake sakin fina-finai barkatai ba tare da cika ƙa’idar da doka ta tanadar musu ba, na kawo kowanne Fim gabanta a tantance shi kafin ya isa ga idanun al’umma inda ta dakatar da cigaba da haska wasu Manyan Fina-finai har guda 22.

Abba El-mustapha ne ya bayyana wannan mataki biyo bayan tattaunawa da manyan jami’an hukumar tare da dogon nazari domin kawo ƙarshen ƙorafe-ƙorafen da yace hukumar ke yawan karɓa don ƙara inganta aiyukan hukumar tare da masana’antar Kannywood, sanarwar tace hukumar ba zata lamunci karan tsaye akan harkar Fim ba a jihar Kano ba.

  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Ya ƙara da cewa doka ce ta bawa hukumar damar tace duk wani Fim tare da lura da aiyukan yan masana’antar Kannywood matsawar suna da rijista da hukumar a ko ina suke, saboda haka ana shawartar masu ɗaukar nauyin waɗannan fina-finai da su tabbatar da sun bi wannan doka ta dakatarwa tare da tsayar da saka waɗannan fina-finai a gidajen TV ko kafar intanet.

Haka kuma ana sanar da su cewa su miƙo fina-finansu ga hukumar domin tantance su tare da ba su shaidar inganci ta tacewa nan da sati ɗaya mai zuwa domin guje wa fushin doka.

Daga ƙarshe hukumar ta nemi haɗin kan dukkannin gidajen TV da hukumar da ke lura da kafafen yaɗa labarai ta Nijeriya wato NBC kan su cigaba da taimaka mata wajen samun nasarar abinda ta saka a gaba da cigaban Jihar Kano da masana’antar Kannywood.

Labarai Masu Nasaba

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Babu Wanda Ya Jawo Ra’ayina  Zuwa Masana’antar Kannywood —Umar Hassan (2)

jami’in yaɗa labaran hukumar Abdullahi Sani Suleiman ya bayyana fina-finan da aka dakatar kamar haka:

1. Dakin Amarya  

2. Mashahuri  

3. Gidan Sarauta  

4. Wasiyya  

5. Tawakkaltu  

6. Mijina  

7. Wani Zamani  

8. Labarina  

9. Mallaka  

10. Kudin Ruwa  

11. Boka Ko Malam  

12. Wa yasan Gobe  

13. Rana Dubu  

14. Manyan Mata  

15. Fatake  

16. Gwarwashi  

17. Jamilun Jiddan  

18. Shahadar Nabila  

19. Dadin Kowa  

20. Tabarma

21. Kishiyata

22. Rigar Aro


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hausa Filmkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Next Post

Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri

Related

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa
Nishadi

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

6 days ago
Hukuma
Nishadi

Babu Wanda Ya Jawo Ra’ayina  Zuwa Masana’antar Kannywood —Umar Hassan (2)

2 weeks ago
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

3 weeks ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

3 weeks ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

4 weeks ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

1 month ago
Next Post
Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri

Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.