• English
  • Business News
Friday, June 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Kano Sun Shirya Fita Zabe Duk Da Rade-Radin Samun Tashin Hankali

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Jama’ar Kano Sun Shirya Fita Zabe Duk Da Rade-Radin Samun Tashin Hankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’ar Jihar Kano sun bayyana shirinsu na yin tururuwa domin fita zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da za yi a ranar Asabar 18 ga watan Maris, 2023.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake rade-radin cewa za a iya samun tashe-tashen hankula a lokacin zaben saboda farin jinin da akalla jam’iyyun siyasa biyu ke da shi na neman kujerar gwamna a jihar.

  • Karancin Kudi: Mun Yi Asarar Kwai Na Biliyan 30 -Masu Kiwo
  • Rikicin Zabe: Jihohin 7 Da Idanuwa Ke Kansu A Zaben Gwamnoni

Wasu daga cikin wadanda za su kada kuri’a wadanda Wakilinmu ya ji ra’ayoyinsu a ranar Juma’a, suna da ra’ayin cewa ba tare da la’akari da abin da ake fada ba za su fita don yin zabe.

Wakilinmu da ya zagaya birnin Kano domin jin ra’ayoyin mazauna garin, ya kuma ruwaito cewa, akwai kwanciyar hankali yayin da ake gudanar da harkokin kasuwanci na yau da kullum.

Ya kuma ruwaito cewar jami’an tsaro a shirye suke da suke yayin da suke sintiri a fadin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Wasu da suka zanta da LEADERSHIP amma ba su ambaci sunayensu na ganin cewa takarar gwamna za ta kasance tsakanin ‘yan takarar jam’iyyar APC, Nasir Yusuf Gawuna, da na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusif.

Malam Tijjanni Abdulrahman, wanda ya zanta da wakilinmu ya ce: “Mun shirya tsaf domin kada kuri’ar ‘yan takarar da muke so, jita-jitar cewa za a yi tashin hankali shi ne a tsoratar da mu daga fitowa amma hakan ba zai hana mu fita ba.”

Mista Chinedu Ogochukwu ya kuma ba da tabbacin cewa shi da iyalansa wadanda suka kai shekarun kada kuri’a za su fito domin kada kuri’a amma za su yi hakan cikin taka-tsan-tsan, ya kara da cewa, “muna jin rade-radin yiwuwar tashin hankali nan da can amma za mu fara duba lamarin tukuna.

Wata mace da ta amince ta yi magana da LEADERSHIP bisa sharadin sakaya sunanta, ta kuma ce za ta fita domin kada kuri’a, amma ba za ta bayyana wanda za ta zaba ba.

Siyasar Kano dai ta dauki zabi, inda manyan jam’iyyun adawa na APC da NNPP ke kokarin kafa gwamnati a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCJami'an TsarokanoNNPPZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Kasar Sin Kan Zamanantarwa

Next Post

Akwai Jan Aiki A Gaban Tinubu – Kungiyar Dattawan Arewa

Related

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

6 hours ago
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

7 hours ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

9 hours ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

1 day ago
Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

1 day ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

1 day ago
Next Post
Akwai Jan Aiki A Gaban Tinubu – Kungiyar Dattawan Arewa

Akwai Jan Aiki A Gaban Tinubu – Kungiyar Dattawan Arewa

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

June 13, 2025
Dawanau

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

June 13, 2025
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

June 13, 2025
Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

June 13, 2025
Gwamna Bala

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi

June 13, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

June 13, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

June 13, 2025
gombe

Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran

June 13, 2025
Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

June 13, 2025
Kano

Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.