ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar LP Ta Kori Dan Takarar Gwamnanta Na Kano, Bashir I. Bashir Daga Jam’iyyar 

by Sadiq
3 years ago
Jam'iyyar LP

Jam’iyyar LP a Jihar Kano, ta yi watsi da ikirarin cewa Bashir Ishak Bashir, wanda ya koma jam’iyyar APC ne dan takararta na gwamna a Jihar.

A ranar Litinin din da ta gabata ne Ishak-Bashir ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) cewa ya fara tattaunawa da jam’iyyar APC domin mara mata baya a zabe mai zuwa.

  • ‘Yansanda Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 15 Da Aka Sace A Anambra
  •  Tsoffin Kudi: Kotun Koli Ta Dage Sauraren Shari’ar Zuwa 22 Ga Fabrairu

“Ina tattaunawa da shugabannin jam’iyyar APC a matakin kasa kan yadda za mu mara wa jam’iyyar baya ta lashe zabe mai zuwa.

ADVERTISEMENT

Ishak-Bashir ya shaida wa NAN cewa: “Ba da jimawa ba zan tuntube ku kan matsayarmu ta karshe kan lamarin. Shugaban jam’iyyar LP a jihar, Alhaji Mohammed Raji, ya yi watsi da ikirarin Ishak-Bashir, inda ya bayyana cewa ba shi ne dan takarar gwamnan LP a jihar ba.

Raji ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a ranar Litinin a Kano cewa, sunan Ishak-Bashir bai taba shiga jadawalin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ba a matsayin dan takarar gwamna na LP a Jihar Kano.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

“Ya zo jam’iyyar shi kadai ya bar jam’iyyar ba tare da kowa ba,” in ji Raji.

Ya kara da cewa tsarin jam’iyyar ya ci gaba da kasancewa tare da dukkan ‘yan takararta na Sanata, Wakilai da na Majalisar Jiha da ke takara a babban zabe mai zuwa.

Sai dai ya ce akwai batutuwa a cikin jam’iyyar da suka haifar da rashin hadin kai a cikin manyan mukamai da mambobin jam’iyyar.

Raji ya kara da cewa “Wasu abubuwan da ba daidai ba” sun yi kokarin karkatar da hankalin jam’iyyar tare da yin barazanar sauya sheka.

“Muna ba da shawara sosai ga irin wadannan nau’ikan mutane da su sani cewa mu ‘Masu biyayya’ muna goyon bayan takarar Obi da Dati dari bisa dari a Jihar Kano,” in ji shi.

A halin da ake ciki, wata majiya a jam’iyyar ta ce an mika sunan Raji ga INEC a matsayin dan takarar gwamna na LP a Jihar Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Next Post
Canjin Kudi: Buhari Ya Yi Ganawar Sirri Da Emefiele

Kin Bin Umarnin Kotu Kan Batun Canjin Kudi Zai Iya Kawo Koma Baya - Masana

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.