• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jamus Za Ta Zuba Jari A Harkar Noma, Kasuwanci Da Lantarki A Jihar Inugu

by Sulaiman and Bello Hamza
1 year ago
Zuba jari

Gwamnatin kasar Jamus ta bayyana aniyarta ta karfafa dangantakar tattalin arzki da gwamati da kuma al’ummar Jihar Inugu, musamman a bangaren harkar gona, lantarki kasuwanci da zuba jari.

 

Ta kuma ce, ta zabi Jihar Inugu ne a matsayin wurare uku da za ta mayar da hankalin ta don zuba jari da gudanar da harkokin kasuwanci a yankin kudancin kasar nan saboda yaddd ta lura da harkokin kasuwanci da zuba jari ke tafiya a karkashin gwamnan jihar Dakta Peter Mbah.

  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

Jakadan kasar Jamus a Nijeriya, Weert Börner, ya bayyana haka yayin da ya jagoranci tawagar ‘yan kasuwa da kwararrun kasar a ziyarar da suka kai wa Gwamna Peter Mbah a garin Inugu.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

Börner ya kuma ce, ziyarar ta kasance ci gaba ne daga tattaunawar da bangarorin suka yi a garin Legas a shekarar 2023, inda aka nemi a kara samar da hadin gwiwa domin bunkasa zumuncin da ke tsakanin bangarorin biyu.

 

“Na yi murnar kasancewa a Inugu domin zurfafa tattaunawarmu, na yi murnar kasacewar cikin tawagar mu a kwai wakilin cibiyar masa’anantun mu (DHK Deutsche Handels Kompetenz), da manyan kamfanoni da suka dade suna harkokin ci gaba a Nijeriya, kamar GIZ da Siemens Energy.

 

“Mun samu labarai daga kafafen sadarwa na Nijeriya wadanda ke nuna cewa, Jihar Inugu ta samar da yanayi mai inganci na zuba jari ga ‘yan kasuwan ciki da kasashen waje.

 

“Gwamnatin Jamus ta yanke shawarar mayar da hankali ga wasu jihohi na musamman a fadin Nijeriya, jihohin sun kuma hada da Ogun, Abia, da Jihar Inugu, a kan haka muka zo nan yau domin tabbatar da wannan shawarar,” in ji Jakadan.

 

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah ya mika godiyarsa ga tawagar kasa Jamus a kan yadda suka zabi jihar sa don gudanar da wannan harkokin bunkasa kasa. Ya yi alkawarin bayar da dukkan goyon baya da suka kamata don samun nasarar da ake bukata, ya kuma ce, dukkan bangarorin za su amfana da huldar da za su a tsakanin su a harkar gona, wutar lantar, kasuwanci wanda hakan zai taimaka wajen samar wa da matasan jihar ayyukan yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kungiyar Houthis Ta Girmama Hakkin Zirga-zirga A Tekun Maliya

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kungiyar Houthis Ta Girmama Hakkin Zirga-zirga A Tekun Maliya

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.