ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karbar Haraji Mai Yawa Ne Ya Durkusar Da Masana’antu A Nijeriya – Kwamiti

by Sadiq
2 years ago
Haraji

Kwamitin shugaban kasa kan inganta karbar haraji da dokokin kudi ya shawarci gwamnatin Nijeriya da ta zabtare wasu jerin haraji har 190 da ake karba daga hannun talakawan kasar nan.

Wannan dai ta zama wata hanya da za a bi wajen sakarwa masu kamfanonin da masana’antu mara, ta yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu da kuma samun riba cikin sauki.

  • Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Alhamis Don Yanke Hukunci Kan Zaben Shugaban Kasa
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Fika Ya Rasu Yana Da Shekara 90

A cikin wani rahoto bayan bincike da kwamitin ya gabatar wa shugaba Tinubu, ya zargi jihohi da karbar harajin da ya wuce kima, kuma bisa rashin ka’ida.

ADVERTISEMENT

Rahoton kwamitin ya ce wannan harajin barkatai da jihohi ke karba, shi ne sanadin tashin farashin kayayyaki da rashin samun ribar da ta dace da kuma lalacewar darajar Naira da sauran matsaloli.

Kwamitin ya yi misali da korafin da kamfanonin sadarwa suka jima suna yi game da yadda jihohi suka mayar da su saniyar tatsa ta yadda suke karbar jerin haraji.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Yayin da yake gabatar da korafin kamfanonin sadarwar, shugaban kungiyar kamfanonin, Gbolahan Awonuga ya ce kowanne kamfanin sadarwa yana biyan haraji daban-daban har guda 40 ko sama da haka duk wata, abin da ya ce yana haddasa musu karancin abokan ciniki saboda tsada.

Shugaban kwamitin shugaban kasa Mista Taiwo Oyedele ya ce kwamitin na shawartar gwamnatin tarayya ta hade haraji fiye da 200 daban-daban da masu kamfanoni ke biya zuwa 10.

Kwamitin ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta yi gaggawar mayar da hankalin kan fannin tattalin arziki, don shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki da kuma lalacewar darajar Naira.

Ana ci gaba da kokawa kan yadda farashin kayan masarufi ke yin tashin gwauron zabi, lamarin da ya sanya dubban mutane gaza cin abinci sau uku a rana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.