Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Karuwar Korona: Gombe Ta Bukaci Jama’a Da Su Bi Dokokin Kariya

by Khalid Idris Doya
December 20, 2020
in LABARAI
2 min read
Ranar Yaki Da Kanjamau
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kwamitin yaki da cutar Korona a jihar Gombe ya yi gargadi ga al’umman jihar game da bin ka’idojin da matakan kariya daga cutar mai hanzarin illata mutane, a daidai gabar da da adadin masu mutuwa daga cutar ke karuwa.

Wannan kiranyen ya biyo bayan fuskantar bukukuwan kirisimeti ne da na sabuwar shekara tare kuma da lura da yadda cutar take kara bazuwa sannu a hankali.

samndaads

Shugaban kwamitin dakile yaduwar cutar a jihar Gombe Dakta Manasseh Daniel Jatau wanda shine mataimakin gwamnan jihar, ya shawarci al’ummar jihar da su bi ka’idojin kariyan kai daga cutar.

Dakta Jatau ya bayyana hakan ne yayin zantawa da manema labarai game da sake barkewar cutar karo na biyu, yana mai cewa an gano karuwar adadin masu dauke da cutar dama masu mutuwa sanadiyyar ta a jihar.

Ya ce zanga-zangar EndSARS da aka yi kwanakin baya a fadin kasar nan ma ya taimaka wajen yaduwar cutar ta korona.

Sai ya bukaci al’ummar jihar da su dauki dabi’ar bin ka’idojin gujewa yaduwar cutar da suka hada da sanya kyallen rufe hanci da baki da wanke hannu da barin tazara a tsakani.

“Mun kira ku ne, ku ‘yan jaridu don yi muku bayani kan ayyukan kwamitin tare da neman hadin kan ku don isar wa al’umma kan bukatar kowa ya bi kaidojin kare kai daga cutar Korona musamman ma a wannan lokaci na bukukuwa da tarukan shagulgula”.

Shi ma Kwamishinan lafiya na jihar, Dakta Ahmad Muhammad Gana ya bayyana cewa, cutar tafi kamari a wannan yanayin na sanyi.

“Abun da ba a son ji ne amma gaskiyar batun shi ne Jihar Gombe tana fuskantar barkewar cutar Korona da yawaitar mace-mace. Muna bukatar jama’a su san da hakan kana su dauki shawarorin da muke bayarwa domin kariya daga wannan lamarin.”

Daga nan Dr. Gana ya bukaci al’umma su bi ka’idojin kariya daga cutar, tare da gujewa karyata samuwar cutar.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Tawagar Sarkin  Kauran Namoda Hari A Funtuwa   

Next Post

Hisbah Za Ta Hana Taron Fati Da Daddare A Kano

RelatedPosts

NIS Ta Kaddamar Da Sansanin Karfafa Tsaron Iyakar Kasa Na 15 A Jihar Ogun

NIS Ta Kaddamar Da Sansanin Karfafa Tsaron Iyakar Kasa Na 15 A Jihar Ogun

by Khalid Idris Doya
13 mins ago
0

A kokarinta na tabbatar da tsaron iyakokin kasar nan, Hukumar...

Sakataren Lamurran Sirri Na Gwamnan Bauchi Ya Yi Murabus

Sakataren Lamurran Sirri Na Gwamnan Bauchi Ya Yi Murabus

by Khalid Idris Doya
3 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Rahotonnin da suke fitowa daga fadar...

Tattabaru

Abin DaYa Sa Tattabarun Da Buhari Ya Saki Ba Su Tashi Ba – Adesina

by Khalid Idris Doya
4 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa...

Next Post
Hisbah

Hisbah Za Ta Hana Taron Fati Da Daddare A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version