Kasar Sin ta yanke shawarar bayar da agajin gaggawa ga kasashen Iran da Jordan da Lebanon da Iraqi da nufin saukaka matsalar jin kai da al’ummomin kasashen ke fuskanta.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian ne ya bayyana haka a yayin taron manema labaru da aka shirya a yau, inda ya ce rikicin da ke gudana ya haifar da matsalar jin kai ga al’ummomin Iran da na sauran kasashen yankin. Yana cewa, Sin na jajantawa jama’ar kasashen da rikicin ya shafa, kuma tana tausaya musu.
Ya kara da cewa Sin za ta ci gaba da yin bakin kokarinta wajen inganta zaman lafiya da dakatar da bude wuta da lalubo hanyoyin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tun da wuri da kuma kare matsalar jin kai daga bazuwa. (FMM)













Discussion about this post