• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Yawan Makamai Masu Linzamin Da Koriya Ta Arewa Ta Mallaka?

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Ko Kun San Yawan Makamai Masu Linzamin Da Koriya Ta Arewa Ta Mallaka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Koriya ta Arewa ta harba abin da ake zargi makami ne mai linzami ya wuce ta sararin saman Japan, wanda ya yi tafiyar kusan kilomitta 500 kafin ya fada Tekun Pacific.

Dama Koriya ta Arewa ta jima tana gwajin makamai masu linzami a shirinta na mallakar muggan makamai, to amma wannan shi ne na farko da ta harba ya bi ta samaniyar Japan tun 2017.

  • Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Ga abin da muka sani game da karfin kasar a fannin makami mai linzami.
Wadanne makamai masu linzami Koriya ta Arewa ke gwaji?

Koriya ta Arewa ta yi gwajin makamai masu linzami sama da 30 a shekarar nan, inda wasu daga cikinsu suke da karfin da za su iya cin dogon zangon da ya kai har Amurka.
Daya daga cikin makaman yana da sauri kamar na sauti kuma a kasa-kasa ta yadda na’urar gano makamai ba za ta iya ganinsa ba.

Ana ganin makamin da ta gwada kwanan nan, wanda ya bi ta saman Japan yana iya cin zangon da ya kai nisan kilomita 4,500 – nisan da zai iya kai wa har tsibirin Guam na Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Haka kuma Koriya ta Arewar na gwajin makami mai linzami samfurin Hwasong-14, wanda ke iya cin nisan zangon kilomita 8,000. Koda yake wasu nazarce-nazarcen na nuni da cewa zai iya cin nisan har kilomita 10,000, abin da hakan ke nufin zai iya kai wa har New York idan aka harba shi daga Koriya ta Arewa.

Wannan ne makami mai linzami na kasar na farko wanda zai iya tafiya daga wata nahiya zuwa wata nahiya.

Ana ganin makami mai linzamin da kasar ta kera tare da gwajinsa kwanan nan, mai suna Hwasong-15 yana iya tafiyar nisan kilomita 13,000, wanda hakan ke nufin zai iya kai wa dukkanin fadin kasar Amurka.

A watan Oktoba na 2020, Koriya ta Arewa ta bayyana makaminta mai linzami na baya-bayan nan mai suna Hwasong-17.
Shi kuwa ana ganin zai iya cin dogon zangon da ya kai kilomita 15,000 ko fi.

Zai kuma iya daukar dunkulen makami har guda uku ko hudu, a lokaci daya maimakon daya kawai, wanda hakan zai sa abu ne mai wuya wata kasa ta iya kare kanta daga makamin.

Kwararru sun ce kaddamar da sabbin makaman masu linzami da Koriya ta Arewa ke yi nuni ne ga gwamnatin Biden ta Amurka na irin karfin da kasar ke ci gaba da samu na soji.

A watan Maris na 2021, ta yi gwajin na’ura mai linzami da za ta iya dako da harba makami mai nauyin tan biyu da rabi, wanda hakan ke nufin zai iya daukar makamin nukiliya kenan.

Masu nazari a cibiyar hana bazuwar makaman nukuliya ta ‘James Martin Center for Nonproliferation Studies,’ sun sheda wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan makami kusan sabon samfuri ne da aka inganta na KN-23 wanda kasar ta taba gwada wa a baya.

Wadanne makaman nukiliya kasar ta mallaka?
Lokaci na karshe da Koriya ta Arewa ta yi gwajin wani bam na nukiliya shi ne a 2017.
Fashewar da aka gani a wurin gwajin makamanta na Punggye-ri ta kai karfin kiloton 100-370.

Bam mai nauyin kiloton 100 ya ninka wanda Amurka ta jefa a birnin Hiroshima a 1945 ninki shida.
Koriya ta Arewa ta yi ikirarin cewa wannan shi ne bam dinta na nukiliya na farko, wanda shi ne mafi karfi a tsakanin dukkanin makaman nukiliya.

Sai dai kuma watakila kasar za ta yi kokarin gwajin wasu kananan makaman na nukiliya da ba su kai wancan karfi ba, in ji kwararre a cibiyar nazarin makamai ta Royal United Serbices Institute, Joseph Byrne.

A ina za ta iya gwajin makaman nukiliya?
Kasar ta yi gwajin makaman nukiliya a karkashin kasa sau shida a wurin gwajinta na Punggye-ri. Sai dai a 2018 Koriya ta Arewa ta ce za ta rufe wurin, saboda ta yi gwajin karfinta na nukiliya. Hukumomin Kasar ta Koriya ta Arewa sun gayyaci ‘yan jarida na waje inda suka lalata wurin a gabansu.

Sai dai abin da ba a sani ba shi ne ko kasar ta lalata wurin yadda ba za a iya sake amfani da shi ba ko kuma ba ta yi hakan ba.
Wasu hotunan tauraron dan-Adam da aka fito da su a shekarar nan sun nuna alamun cewa ana sake gyara wurin. Duk wani gwaji da za a yi a wurin zai saba yarjejeniyar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Farfado da cibiyar hada makamanta na nukiliya
A shekara ta 2018, shugaban Koriya ta Arewar Kim Jong-un ya yi wa shugaban Amurka na lokacin Donald Trump alkawarin cewa, zai lalata dukkanin cibiyoyin kasarsa na hada makaman nukiliya.

Sai dai hukumar nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce wasu hotunan tauraron dan-‘Adam sun nuna alamun cewa, kasar ta sake farfado da cibiyarta ta hadawa tare da inganta sinadarin hada makamin nukiliya.

Mun ciro daga BBC HAUSA


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 11, Ya Jikkata 8 A Bauchi

Next Post

Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

6 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

7 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

1 week ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.