ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Yawan Makamai Masu Linzamin Da Koriya Ta Arewa Ta Mallaka?

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Koriya

Koriya ta Arewa ta harba abin da ake zargi makami ne mai linzami ya wuce ta sararin saman Japan, wanda ya yi tafiyar kusan kilomitta 500 kafin ya fada Tekun Pacific.

Dama Koriya ta Arewa ta jima tana gwajin makamai masu linzami a shirinta na mallakar muggan makamai, to amma wannan shi ne na farko da ta harba ya bi ta samaniyar Japan tun 2017.

  • Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Ga abin da muka sani game da karfin kasar a fannin makami mai linzami.
Wadanne makamai masu linzami Koriya ta Arewa ke gwaji?

ADVERTISEMENT

Koriya ta Arewa ta yi gwajin makamai masu linzami sama da 30 a shekarar nan, inda wasu daga cikinsu suke da karfin da za su iya cin dogon zangon da ya kai har Amurka.
Daya daga cikin makaman yana da sauri kamar na sauti kuma a kasa-kasa ta yadda na’urar gano makamai ba za ta iya ganinsa ba.

Ana ganin makamin da ta gwada kwanan nan, wanda ya bi ta saman Japan yana iya cin zangon da ya kai nisan kilomita 4,500 – nisan da zai iya kai wa har tsibirin Guam na Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Haka kuma Koriya ta Arewar na gwajin makami mai linzami samfurin Hwasong-14, wanda ke iya cin nisan zangon kilomita 8,000. Koda yake wasu nazarce-nazarcen na nuni da cewa zai iya cin nisan har kilomita 10,000, abin da hakan ke nufin zai iya kai wa har New York idan aka harba shi daga Koriya ta Arewa.

Wannan ne makami mai linzami na kasar na farko wanda zai iya tafiya daga wata nahiya zuwa wata nahiya.

Ana ganin makami mai linzamin da kasar ta kera tare da gwajinsa kwanan nan, mai suna Hwasong-15 yana iya tafiyar nisan kilomita 13,000, wanda hakan ke nufin zai iya kai wa dukkanin fadin kasar Amurka.

A watan Oktoba na 2020, Koriya ta Arewa ta bayyana makaminta mai linzami na baya-bayan nan mai suna Hwasong-17.
Shi kuwa ana ganin zai iya cin dogon zangon da ya kai kilomita 15,000 ko fi.

Zai kuma iya daukar dunkulen makami har guda uku ko hudu, a lokaci daya maimakon daya kawai, wanda hakan zai sa abu ne mai wuya wata kasa ta iya kare kanta daga makamin.

Kwararru sun ce kaddamar da sabbin makaman masu linzami da Koriya ta Arewa ke yi nuni ne ga gwamnatin Biden ta Amurka na irin karfin da kasar ke ci gaba da samu na soji.

A watan Maris na 2021, ta yi gwajin na’ura mai linzami da za ta iya dako da harba makami mai nauyin tan biyu da rabi, wanda hakan ke nufin zai iya daukar makamin nukiliya kenan.

Masu nazari a cibiyar hana bazuwar makaman nukuliya ta ‘James Martin Center for Nonproliferation Studies,’ sun sheda wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan makami kusan sabon samfuri ne da aka inganta na KN-23 wanda kasar ta taba gwada wa a baya.

Wadanne makaman nukiliya kasar ta mallaka?
Lokaci na karshe da Koriya ta Arewa ta yi gwajin wani bam na nukiliya shi ne a 2017.
Fashewar da aka gani a wurin gwajin makamanta na Punggye-ri ta kai karfin kiloton 100-370.

Bam mai nauyin kiloton 100 ya ninka wanda Amurka ta jefa a birnin Hiroshima a 1945 ninki shida.
Koriya ta Arewa ta yi ikirarin cewa wannan shi ne bam dinta na nukiliya na farko, wanda shi ne mafi karfi a tsakanin dukkanin makaman nukiliya.

Sai dai kuma watakila kasar za ta yi kokarin gwajin wasu kananan makaman na nukiliya da ba su kai wancan karfi ba, in ji kwararre a cibiyar nazarin makamai ta Royal United Serbices Institute, Joseph Byrne.

A ina za ta iya gwajin makaman nukiliya?
Kasar ta yi gwajin makaman nukiliya a karkashin kasa sau shida a wurin gwajinta na Punggye-ri. Sai dai a 2018 Koriya ta Arewa ta ce za ta rufe wurin, saboda ta yi gwajin karfinta na nukiliya. Hukumomin Kasar ta Koriya ta Arewa sun gayyaci ‘yan jarida na waje inda suka lalata wurin a gabansu.

Sai dai abin da ba a sani ba shi ne ko kasar ta lalata wurin yadda ba za a iya sake amfani da shi ba ko kuma ba ta yi hakan ba.
Wasu hotunan tauraron dan-Adam da aka fito da su a shekarar nan sun nuna alamun cewa ana sake gyara wurin. Duk wani gwaji da za a yi a wurin zai saba yarjejeniyar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Farfado da cibiyar hada makamanta na nukiliya
A shekara ta 2018, shugaban Koriya ta Arewar Kim Jong-un ya yi wa shugaban Amurka na lokacin Donald Trump alkawarin cewa, zai lalata dukkanin cibiyoyin kasarsa na hada makaman nukiliya.

Sai dai hukumar nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce wasu hotunan tauraron dan-‘Adam sun nuna alamun cewa, kasar ta sake farfado da cibiyarta ta hadawa tare da inganta sinadarin hada makamin nukiliya.

Mun ciro daga BBC HAUSA

Koriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.