Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Korona: Jihar Kwara Ta Kakaba Kulle Mai Sauki

by Muhammad
December 24, 2020
in LABARAI
2 min read
Kwara
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
  • Ma’aikatan Jihar Za Su Rika Aiki Daga Gida

Daga Khalid Idris Doya,

 

samndaads

Bisa barkewar annobar Korona karo na biyu, Gwamnatin Jihar Kwara a jiya Laraba ta kulle jihar, amma kulle wanda ba mai tsanani ba, domin kare jama’an jihar daga yaduwar cutar.

Umarnin kulle zai fara aiki ne daga yau Alhamis 24 ga watan Disamban 2020 har zuwa nan da mataki na gaba kuma.

Mataimakin Shugaban kwamitin yaki da korona a jihar, Razak Raji ya shaida wa ‘yan jarida a Illorin cewa amfani da takunkumin rufe hanci da baki a cikin jama’a ya zama dole a fadin jihar, inda ya kara da cewa dukkanin wani tarukan jama’a da bukukuwan da ke haifar da cunkoson jama’a an dakatar da shi har zuwa nan da wani lokaci.

“Wuraren ibada ba a amince musu su hadu a lokaci guda sama da kashi 50 na girman wajensu ba. Wannan zai bada dama a samu bada tazara da kiyaye ka’idar rage cinkoson jama’a.

“Dukkanin wani taron da zai hada mutum sama da 50 ba a amince da yin sa ba. Sannan wurare su sanya matakin in babu takunkumin rufe fuska da hanci to kada su bar mutum ya shiga.”

Raji, wanda kuma shine kwamishinan lafiya na jihar, ya kara da cewa, “Ma’aikata an umarce su da suke gudanar da ayyukansu daga gida. Ma’aikatan da ke bakunan ayyukan musamman ne kawai aka amince su cigaba da gudanar da ayyukansu yadda suka saba musamman ma’aikatan lafiya. Ganawa ta bidiyo shine abun da ya fi dacewa a yanzu.”

“A bangaren sufuri, an bada umarnin dole direbobi da fasinjoji da su ke amfani da kyallen rufe hanci da baki. Akwai hukunci da ladaftarwa ga dukkanin wadanda suka karya dokokin da aka sanya.

“An samar da jami’an tsaron da za su tabbatar an bi dokoki da ka’idojin da aka sanya domin tabbatar da jama’a sun bi matakan kariya. Wadanda suka karya dokar da aka sanya su na barazana wa lafiyar jama’a.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Rattaba Hannu A Kasafin 2021 Na Biliyan N120.3

Next Post

DSS Ta Fadakar Da ’Yan Nijeriya Shirin Tada Boma-bomai A Wuraren Cunkoso

RelatedPosts

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Rasuwar

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mai Shari’ a Rabiu Danlami A Kano

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Haruna Akarada, Ana cigaba da gudanar da ta’aziyya ta...

Next Post
DSS

DSS Ta Fadakar Da ’Yan Nijeriya Shirin Tada Boma-bomai A Wuraren Cunkoso

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version