ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Masu Masana’antu Ta Samu Bashin Naira Biliyan 75 Daga Bankin BOI

by Abubakar Abba
1 year ago
BOI

Bankin masana’antu, BOI ya bai wa kungiyar matsakaitan masu masana’antu ta kasa NASSI, bashin Naira biliyan 75.

Ya bai wa kungiyar bashi ne, domin ta tallafa wa ‘ya’yan kungiyar a kan sana’oinsu da suke gudanarwa.

  • Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano
  • An Watsa Shirin Bidiyo Zagaye Na 3 Mai Taken “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” A Rasha

An wanzar da rabbata hannun bayar da bashin ne, ta hanyar sanya hannu a tsakanin shugaban kungiyar na kasa Dakta Solomon Daniel Bonfa da kuma manajin darakta na bankin na masana’antu, Dakta Olasupo Olusi.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa a kan shirin Ma’ajiyin kungiyar na kasa Dakta Abubakar Tanko Bala, ya bayyana cewa, an tsari bashi ne, zuwa kashi uku.

A cewarsa, manyan masu gudanar da masana’antu, za su samu bashin Naira biliyan 75, inda kuma kanannan masu matsakaitan sana’oi, suma za su samu irin yawan wannan adadin kudin.

LABARAI MASU NASABA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Ya kara da cewa, wadanda ke a kan tsarin kasuwanci na Nano, za su samu bashin Naira biliyan 50.

Bala ya kuma gode wa kokarin da mankin na BOI ke ci gaba da yi, wajen kara tabbatar da wanzar da bayar da bashin.

Ya bayyana cewa, kungiyar na kuma ci gaba da gamgamin fadakar da kai ga masu gudanar da kanannan sana’oi a daukacin fadin kasar nan, musamman a kan yadda za su ci gaba da gudanar da ayyukansu na kasuwanci don su san mahimmancin bashin da aka ba su.

Ya kara da cewa, wannan shirin, ya nuna a zahiri, na jajircewar gwamnatin shugaban kasa mahimmancin Bola Ahmed Tinubu, na yunkurin magance kalubalen da tattalin arzkin Nijeriya ke fuskanta da kuma tallafawa ‘yan kasuwa, don su tsaya a kan kafafunsu.

Ya bukaci ‘ya’yan kungiyar da ke a fadin kasar, da su shiga cikin shirin domin su amafana su kuma bayar da ta su gudunmawar, waen kara habaka tattalin arzkin kasar.

Bala ya bayyana yakininsa na cewa, wadanda suka amfana da bashin, za su yi amfani da shi yadda ya dace da kuma mai do da bashin, musamman domin a ci gaba da gudanar da shirin har zuwa na dogon zango.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
Tattalin Arziki

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Amfani Da Jarin Waje Da Ya Kai Yuan Biliyan 640.6 Tsakanin Janairu Zuwa Satumban Bana

Sin Ta Yi Amfani Da Jarin Waje Da Ya Kai Yuan Biliyan 640.6 Tsakanin Janairu Zuwa Satumban Bana

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.