Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar NASFAT Ta Shawarci Shugabannin Nijeriya

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
Kungiyar NASFAT Ta Shawarci Shugabannin Nijeriya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Babban Malami mai wa’azi na kungiyar, Nasrullah -il fatih (NASFAT), Imam Abdul-Azeez Onike, ya shawarci shugabannin siyasa da na Addini da su guji yin kalaman kiyayya, a maimakon hakan, su rungumi junansu.
Onike ya bayar da wannan shawarar ce cikin wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na kasa ya yi da shi ranar Juma’a a Legas, a dab da bukin ranar yin hakuri da juna da samar da zaman lafiya ta 16 ga watan Nuwamba.
Tun a shekarar 2018 ne wani shahararren malami, Sheikh Khalifa bin Zayed Al Nahyan, da ke kasar hadaddiyar Daular Larabawa, ya kaddamar da wannan ranar.
Ranar Duniyar ta nuna hakuri da juna wacce UNESCO ta shelanta gabatarwa a duk shekara tun daga shekarar 1995 domin wayar da kan al’ummu a kan hadarin da ke tattare da rashin hakuri da juna. Ana gabatar da ita ne a duk ranar 16 ga watan Nuwamba, na kowace shekara.
Taken ranar shi ne: “Prospering from Pluralism: Embracing Dibersity through Innobation and Collaboration.”
A cewar Onike, rashin hakuri da yin kalaman batunci ba za su amfanar da komai ba, sai dai ma su yi hannun riga da koyarwar Addini.
Ya kuma bukaci mabiya manyan Addinan kasar nan biyu da su kasance masu neman wata mafitar da kuma fahimta mai kyau a duk lokacin da suka yi karo da wani malamin da yake yin wa’azin haifar da rashin hakuri da rashin zaman lafiya.
Onike ya ce, manufar Addinin Musulunci shi ne daukaka abin da zai amfani al’umma da kawar da abin da zai cutar da al’umma.
Ya ce an gina Shari’ar Musulunci ne a kan basira da jin dadin bayin Allah a cikin rayuwar su da kuma bayan mutuwar su.
“Baki-dayan Shari’a adalci ne, tausayi, amfanarwa da kuma basira.
“Duk wani abin da ya saba wa adalci ya zama zalunci, ya saba wa tausayi ya zama mugunta, ya saba wa amfanarwa ya zama barna, ko ya saba wa basira ya zama wawici, sam wannan abin ba a cikin Shari’a ne yake ba, ko da kuwa an yi kokarin shigar da shi ta hanyar tawili.
Ya bukaci ‘yan Nijeriya da su rika tuna sakon da ke cikin ranar ta 16 ga watan na Nuwamba.
An kebe wannan ranar ce domin kara fahimtar juna da girmama juna a tsakankanin al’umma mabambanta fahimta.
“Akwai bukatar yin hakuri da juna a kowane fanni na rayuwa, saboda hakan yana taka mahimmiyar rawa wajen samar da zaman lafiya, kauna da soyayya a cikin al’umma.
“Ya kamata a gane a sarari cewa, girmama juna da yin hakuri da juna ba yana nufin na bar fahimta ta ne ba na komo naka,” in ji shi.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Ware Kaso Mai Tsoka Don Kula Lafiyar Al’umma

Next Post

Ko Kasan Irin Kalubalen Dake Gaban Messi?

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
3 hours ago
0

...

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

by
7 hours ago
0

...

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

by
8 hours ago
0

...

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

by
9 hours ago
0

...

Next Post
Ko Kasan Irin Kalubalen Dake Gaban Messi?

Ko Kasan Irin Kalubalen Dake Gaban Messi?

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: