ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyamar ‘Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Shaye-Shaye

Shugabar Gidauniyar Yaki da Shayeshayen Miyagun Kwayoyi ta Kasa (YADAF), Hajiya Fatima Bature ta bayyana cewa yawaitar matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi da ke kara ta’azzara a tsakanin matasan yana karuwa ne sakamakon kyamatar su da ake yi.

Shugabar YADAF ta bayyana haka a lokacin da take bayyana sabbin tsaretsaren gidauniyar wanda zuwa yanzu ake kan aiwatar da su.

  • Mata A Daina Yawace-yawace Da Shige-shige Mara Amfani -Halima Kassim
  • Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Hajiya Fatima ya ce a lokuta dabandaban bisa bincike da tattaunawar da Gidauniyar YADAF ta gudanar tare da sauraron bayanan wasu masu fama da irin wannan matsala, akwai bukatar jama’a da sauran kungiyoyi su sake dabara ta yadda za a daina kyamatar masu wannan dabi’ar, a ci gaba da jansu a jika tare da sauraron bayanansu, ta haka ne kawai za a iya fahimtar hakikanin matsalolin da ke haifar da ta’azzarar annobar.

ADVERTISEMENT

Ta ci gaba da cewa “Sakamakon binciken da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa da yawa daga cikin masu matsalar shaye-shaye sun tsinci kansu a wannan hali ne sakamakon rikon sakainar kashi da wasu iyayen ke yi wa rayuwar yaransu, wasu kuma kuncin rayuwa, wasu rabuwar iyali, wasu munanan abokai da sauransu.

“Saboda haka ba za a fahimci haka ba sai an daina kyamatar su, an ja masu irin wannan matsala ajiki, sannan za su saki jiki su yi bayanin abin da ya kaisu ga fadawa cikin matsalar.”

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

A karshe Hajiya Fatima ta bukaci malaman Jihar Kano dama kasa baki daya da su yi kokarin shigar da wannan gangami cikin hudubobinsu, domin jama’a a karkara da sauran garuruwan da ke nesa da na kusa su fahimci kyakkawar manufar wannan Gidauniya ta YADAF.

Ta nemi goyon bayan iyayen kasa da malamai a kan lallai su ci gaba aikin da suke yi na wayar da kan al’umma domin kauce wa afkawa cikin wannan ta’ada.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 50, Da Dama Sun Rasa Muhallansu A Jigawa

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 50, Da Dama Sun Rasa Muhallansu A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.