• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyamar ‘Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Kyamar ‘Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabar Gidauniyar Yaki da Shayeshayen Miyagun Kwayoyi ta Kasa (YADAF), Hajiya Fatima Bature ta bayyana cewa yawaitar matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi da ke kara ta’azzara a tsakanin matasan yana karuwa ne sakamakon kyamatar su da ake yi.

Shugabar YADAF ta bayyana haka a lokacin da take bayyana sabbin tsaretsaren gidauniyar wanda zuwa yanzu ake kan aiwatar da su.

  • Mata A Daina Yawace-yawace Da Shige-shige Mara Amfani -Halima Kassim
  • Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Hajiya Fatima ya ce a lokuta dabandaban bisa bincike da tattaunawar da Gidauniyar YADAF ta gudanar tare da sauraron bayanan wasu masu fama da irin wannan matsala, akwai bukatar jama’a da sauran kungiyoyi su sake dabara ta yadda za a daina kyamatar masu wannan dabi’ar, a ci gaba da jansu a jika tare da sauraron bayanansu, ta haka ne kawai za a iya fahimtar hakikanin matsalolin da ke haifar da ta’azzarar annobar.

Ta ci gaba da cewa “Sakamakon binciken da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa da yawa daga cikin masu matsalar shaye-shaye sun tsinci kansu a wannan hali ne sakamakon rikon sakainar kashi da wasu iyayen ke yi wa rayuwar yaransu, wasu kuma kuncin rayuwa, wasu rabuwar iyali, wasu munanan abokai da sauransu.

“Saboda haka ba za a fahimci haka ba sai an daina kyamatar su, an ja masu irin wannan matsala ajiki, sannan za su saki jiki su yi bayanin abin da ya kaisu ga fadawa cikin matsalar.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

A karshe Hajiya Fatima ta bukaci malaman Jihar Kano dama kasa baki daya da su yi kokarin shigar da wannan gangami cikin hudubobinsu, domin jama’a a karkara da sauran garuruwan da ke nesa da na kusa su fahimci kyakkawar manufar wannan Gidauniya ta YADAF.

Ta nemi goyon bayan iyayen kasa da malamai a kan lallai su ci gaba aikin da suke yi na wayar da kan al’umma domin kauce wa afkawa cikin wannan ta’ada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KyamaShaye-ShayeTarbiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saurayi Ya Babbake Gawar Budurwarsa Bayan Dirka Mata Ciki A Bauchi

Next Post

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 50, Da Dama Sun Rasa Muhallansu A Jigawa

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

52 minutes ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

4 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

5 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

7 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 50, Da Dama Sun Rasa Muhallansu A Jigawa

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 50, Da Dama Sun Rasa Muhallansu A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.