• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin LEADERSHIP wallafa jaridar Leadership ta Turanci da Hausa, sun kara karfafa dangantakarsa da kamfanin yada labarai na Kasar Sin (CMG) don fadada aiki tsakanin kamfanonin biyu.

Wannan ci gaban ya samo asali ne lokacin da tawagar CMG karkashin jagorancin babban daraktan cibiyar shirye-shiryen harsunan Asiya da Afirka, An Xiaoyu, ta kai ziyarar aiki hedikwatar kamfanin LEADERSHIP da ke Abuja a ranar Talata.

  • Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF
  • Dokokin Da Buhari Ya Sanya Wa Hannu Kafin Barin Mulki

Sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ke da nufin kawo sabbin matakai da za su amfanar da kamfanonin biyu.

Da take maraba da tawagar CMG, shugabar kamfanin LEADERSHIP Group Limited, Misis Zainab Nda-Isaiah, ta ce ziyarar ta yi daidai domin za ta karfafa hadin gwiwar da ke tsakanin manyan kafafen yada labarai biyu da aka fara a shekarar 2018.

Ta kuma kara da cewa, kamfanin LEADERSHIP na da tsari da hangen nesa don bunkasa ayyukansa, ta kuma bukaci kafar ta kasar Sin da ta taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da dangantakar da ke tsakaninsu zuwa wani mataki.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda A Kano Sun Gargadi Sarki Sanusi Kan Yekuwar Fitowa Hawan Sallah

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Ta ce, “Idan muka sa wannan hadin gwiwa ya kasance mai amfani ta hanyar cika yarjejeniyar da muka yi, jama’armu za su amfana, ba a iya kanmu kadai ba har jikokinmu.”

Dangantakar dai ta fara ne daga wallafa labaran kasar sin a shafin “Daga Sin,” na LEADERSHIP Hausa wanda daga bisani aka samar masa da shafinna musamman q jaridar Hausa mai suna “Baban Bongo”.

Madam Nda-Isaiah ta kuma yaba wa gwamnatin kasar Sin bisa tsauraran ka’idoji da takunkumin da ta dauka kan yada labaran karya.

Ta bayyana cewa hakan zai magance rashin dacewar da wasu shafukan sada zumunta ke yi, da kuma dakile barazanar da labaran karya ke yi wa al’umma.

“Yana da kyau a samar da ka’idoji kan yada labaran karya don magance munanan illolinsa ga al’umma. Yana da kyau gwamnatin kasar Sin ta dauki nauyi,” in ji ta.

Ta kuma ba da tabbacin cewa LEADERSHIP za ta samu lokaci don kai wa CMG ziyara.

A nasa bangaren, Xiaoyu ya ce kofar CMG a bude take ga duk wani nau’in hadin gwiwa daga kamfanin LEADERSHIP, musamman kan kafafen yada labarai.

Ya kuma bayyana cewa, CMG za ta fadada shirye-shiryensa na horas da ma’aikatan LEADERSHIP don samun ci gaba a fannin aikinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlakaCMGDangantakaJaridaLeadership HausaYarjejeniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF

Next Post

Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Biya Bashin Shari’a N226bn, $556.8m, £98.5m

Related

Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargadi Sarki Sanusi Kan Yekuwar Fitowa Hawan Sallah

1 minute ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

3 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

6 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

9 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

10 hours ago
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
Manyan Labarai

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

12 hours ago
Next Post
Ina Neman Gafarar ‘Yan Nijeriya Idan Na Muku Ba Dai-dai Ba —Buhari

Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Biya Bashin Shari'a N226bn, $556.8m, £98.5m

LABARAI MASU NASABA

Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargadi Sarki Sanusi Kan Yekuwar Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.