• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin LEADERSHIP wallafa jaridar Leadership ta Turanci da Hausa, sun kara karfafa dangantakarsa da kamfanin yada labarai na Kasar Sin (CMG) don fadada aiki tsakanin kamfanonin biyu.

Wannan ci gaban ya samo asali ne lokacin da tawagar CMG karkashin jagorancin babban daraktan cibiyar shirye-shiryen harsunan Asiya da Afirka, An Xiaoyu, ta kai ziyarar aiki hedikwatar kamfanin LEADERSHIP da ke Abuja a ranar Talata.

  • Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF
  • Dokokin Da Buhari Ya Sanya Wa Hannu Kafin Barin Mulki

Sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ke da nufin kawo sabbin matakai da za su amfanar da kamfanonin biyu.

Da take maraba da tawagar CMG, shugabar kamfanin LEADERSHIP Group Limited, Misis Zainab Nda-Isaiah, ta ce ziyarar ta yi daidai domin za ta karfafa hadin gwiwar da ke tsakanin manyan kafafen yada labarai biyu da aka fara a shekarar 2018.

Ta kuma kara da cewa, kamfanin LEADERSHIP na da tsari da hangen nesa don bunkasa ayyukansa, ta kuma bukaci kafar ta kasar Sin da ta taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da dangantakar da ke tsakaninsu zuwa wani mataki.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ta ce, “Idan muka sa wannan hadin gwiwa ya kasance mai amfani ta hanyar cika yarjejeniyar da muka yi, jama’armu za su amfana, ba a iya kanmu kadai ba har jikokinmu.”

Dangantakar dai ta fara ne daga wallafa labaran kasar sin a shafin “Daga Sin,” na LEADERSHIP Hausa wanda daga bisani aka samar masa da shafinna musamman q jaridar Hausa mai suna “Baban Bongo”.

Madam Nda-Isaiah ta kuma yaba wa gwamnatin kasar Sin bisa tsauraran ka’idoji da takunkumin da ta dauka kan yada labaran karya.

Ta bayyana cewa hakan zai magance rashin dacewar da wasu shafukan sada zumunta ke yi, da kuma dakile barazanar da labaran karya ke yi wa al’umma.

“Yana da kyau a samar da ka’idoji kan yada labaran karya don magance munanan illolinsa ga al’umma. Yana da kyau gwamnatin kasar Sin ta dauki nauyi,” in ji ta.

Ta kuma ba da tabbacin cewa LEADERSHIP za ta samu lokaci don kai wa CMG ziyara.

A nasa bangaren, Xiaoyu ya ce kofar CMG a bude take ga duk wani nau’in hadin gwiwa daga kamfanin LEADERSHIP, musamman kan kafafen yada labarai.

Ya kuma bayyana cewa, CMG za ta fadada shirye-shiryensa na horas da ma’aikatan LEADERSHIP don samun ci gaba a fannin aikinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlakaCMGDangantakaJaridaLeadership HausaYarjejeniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF

Next Post

Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Biya Bashin Shari’a N226bn, $556.8m, £98.5m

Related

Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 hour ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

4 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

5 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

7 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

21 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

1 day ago
Next Post
Ina Neman Gafarar ‘Yan Nijeriya Idan Na Muku Ba Dai-dai Ba —Buhari

Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Biya Bashin Shari'a N226bn, $556.8m, £98.5m

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.