ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

by Sadiq
2 years ago
Leadership

Kamfanin LEADERSHIP wallafa jaridar Leadership ta Turanci da Hausa, sun kara karfafa dangantakarsa da kamfanin yada labarai na Kasar Sin (CMG) don fadada aiki tsakanin kamfanonin biyu.

Wannan ci gaban ya samo asali ne lokacin da tawagar CMG karkashin jagorancin babban daraktan cibiyar shirye-shiryen harsunan Asiya da Afirka, An Xiaoyu, ta kai ziyarar aiki hedikwatar kamfanin LEADERSHIP da ke Abuja a ranar Talata.

  • Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF
  • Dokokin Da Buhari Ya Sanya Wa Hannu Kafin Barin Mulki

Sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ke da nufin kawo sabbin matakai da za su amfanar da kamfanonin biyu.

ADVERTISEMENT

Da take maraba da tawagar CMG, shugabar kamfanin LEADERSHIP Group Limited, Misis Zainab Nda-Isaiah, ta ce ziyarar ta yi daidai domin za ta karfafa hadin gwiwar da ke tsakanin manyan kafafen yada labarai biyu da aka fara a shekarar 2018.

Ta kuma kara da cewa, kamfanin LEADERSHIP na da tsari da hangen nesa don bunkasa ayyukansa, ta kuma bukaci kafar ta kasar Sin da ta taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da dangantakar da ke tsakaninsu zuwa wani mataki.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Ta ce, “Idan muka sa wannan hadin gwiwa ya kasance mai amfani ta hanyar cika yarjejeniyar da muka yi, jama’armu za su amfana, ba a iya kanmu kadai ba har jikokinmu.”

Dangantakar dai ta fara ne daga wallafa labaran kasar sin a shafin “Daga Sin,” na LEADERSHIP Hausa wanda daga bisani aka samar masa da shafinna musamman q jaridar Hausa mai suna “Baban Bongo”.

Madam Nda-Isaiah ta kuma yaba wa gwamnatin kasar Sin bisa tsauraran ka’idoji da takunkumin da ta dauka kan yada labaran karya.

Ta bayyana cewa hakan zai magance rashin dacewar da wasu shafukan sada zumunta ke yi, da kuma dakile barazanar da labaran karya ke yi wa al’umma.

“Yana da kyau a samar da ka’idoji kan yada labaran karya don magance munanan illolinsa ga al’umma. Yana da kyau gwamnatin kasar Sin ta dauki nauyi,” in ji ta.

Ta kuma ba da tabbacin cewa LEADERSHIP za ta samu lokaci don kai wa CMG ziyara.

A nasa bangaren, Xiaoyu ya ce kofar CMG a bude take ga duk wani nau’in hadin gwiwa daga kamfanin LEADERSHIP, musamman kan kafafen yada labarai.

Ya kuma bayyana cewa, CMG za ta fadada shirye-shiryensa na horas da ma’aikatan LEADERSHIP don samun ci gaba a fannin aikinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Next Post
Ina Neman Gafarar ‘Yan Nijeriya Idan Na Muku Ba Dai-dai Ba —Buhari

Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Biya Bashin Shari'a N226bn, $556.8m, £98.5m

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.