• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF

by Sadiq
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ya ce yakin Sudan ya raba akalla yara 450,000 da gidajensu, tare da haddasa gudun hijira zuwa kasashe makwabta.

Kungiyoyin ba da agaji sun ce ana hana wadannan yaran ‘yan gudun hijira ilimi, tare da fuskantar hatsarin fadawa hannun bata gari, kamar auren yara ko daukar makami don shiga kungiyar ‘yan ta’adda.

  • Kwana 5 Ga Rantsuwa: Waiwaye Kan Rawar Da Matan Shugabannin Kasa Suka Taka A Baya
  • Biden Ya Turo Tawaga Don Halartar Rantsar Da Tinubu

Yayin da dubun dubatan ‘yan gudun hijira ke isa kan iyakar Sudan zuwa Chadi, yawancin taimakon da Majalisar Dinkin Duniya ke bayarwa da kungiyoyin agaji ya mayar da hankali ne kan ruwa da abinci da kuma sauran kayan amfani na yau da kullum ga ‘yan gudun hijira.

Amma ‘yan gudun hijira kamar Abdelnasser Mahamout mai shekaru 18 da haihuwa, sun ce akwai matukar bukatar ilimi.

Yakin basasar Sudan, wanda ya fara a ranar 15 ga Afrilu, ya haifar da rikicin kabilanci a yammacin Darfur.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Dole ta sa ya gudu zuwa Chadi ba tare da iyayensa ba.

Mahamout ya ce tun makonni bai ji daga iyayensa ba, kuma ba shi da masaniyar suna raye ko sun mutu.

Yanzu haka yana zaune a wani karamin sansani tare da ’yan uwansa, kuma ya ce babu wata hanya da zai iya daukar jarabawar shiga Jami’ar Sudan.

Malek Mohammed, malami da ya yi gudun hijira zuwa kasar Chadi daga yammacin Darfur, ya koka da halin kunci da yaran da ya ke koyarwa a baya suke zama a ciki.

Mohammed ya ce malamai na kokarin samar da hanyar da yara za su yi jarabawar Sudan a Chadi.

Gwamnati a Khartoum ta daina aiki tun lokacin da aka fara yakin basasa, don haka da alama ba za a iya daidaitawa ba.

Education Cannot Wait, ECW, ita ce asusun Majalisar Dinkin Duniya don ilimi a lokutan rikici.

Daraktar kungiyar, Yasmine Sherif, ta kai ziyara kasar Chadi a watan Mayu, inda ta yi alkawarin bai wa kasar Chadi dala miliyan uku domin samar da ilimi.

Tasirin yakin Sudan kan yara bai takaita ga ilimi ba kadai.

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar a ranar 12 ga watan Mayu cewa, wata masana’anta ta Sudan da ke samar da kashi 60 cikin 100 na abinci na musamman da ake amfani da su wajen magance matsalar karancin abinci mai gina jiki a kasar an lalata su saboda fadan.

Dubun dubatar yara a Sudan ne za su samu kansu cikin irin wannan hali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FadaRikiciSudanUNICEFYakin BasasaYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokokin Da Buhari Ya Sanya Wa Hannu Kafin Barin Mulki

Next Post

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

Related

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
Kasashen Ketare

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

1 day ago
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

3 days ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

3 days ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

3 days ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

7 days ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

1 week ago
Next Post
LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.