ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadan Sudan Ya Hana Kananan Yara Samun Ilimi —UNICEF

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ya ce yakin Sudan ya raba akalla yara 450,000 da gidajensu, tare da haddasa gudun hijira zuwa kasashe makwabta.

Kungiyoyin ba da agaji sun ce ana hana wadannan yaran ‘yan gudun hijira ilimi, tare da fuskantar hatsarin fadawa hannun bata gari, kamar auren yara ko daukar makami don shiga kungiyar ‘yan ta’adda.

  • Kwana 5 Ga Rantsuwa: Waiwaye Kan Rawar Da Matan Shugabannin Kasa Suka Taka A Baya
  • Biden Ya Turo Tawaga Don Halartar Rantsar Da Tinubu

Yayin da dubun dubatan ‘yan gudun hijira ke isa kan iyakar Sudan zuwa Chadi, yawancin taimakon da Majalisar Dinkin Duniya ke bayarwa da kungiyoyin agaji ya mayar da hankali ne kan ruwa da abinci da kuma sauran kayan amfani na yau da kullum ga ‘yan gudun hijira.

ADVERTISEMENT

Amma ‘yan gudun hijira kamar Abdelnasser Mahamout mai shekaru 18 da haihuwa, sun ce akwai matukar bukatar ilimi.

Yakin basasar Sudan, wanda ya fara a ranar 15 ga Afrilu, ya haifar da rikicin kabilanci a yammacin Darfur.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Dole ta sa ya gudu zuwa Chadi ba tare da iyayensa ba.

Mahamout ya ce tun makonni bai ji daga iyayensa ba, kuma ba shi da masaniyar suna raye ko sun mutu.

Yanzu haka yana zaune a wani karamin sansani tare da ’yan uwansa, kuma ya ce babu wata hanya da zai iya daukar jarabawar shiga Jami’ar Sudan.

Malek Mohammed, malami da ya yi gudun hijira zuwa kasar Chadi daga yammacin Darfur, ya koka da halin kunci da yaran da ya ke koyarwa a baya suke zama a ciki.

Mohammed ya ce malamai na kokarin samar da hanyar da yara za su yi jarabawar Sudan a Chadi.

Gwamnati a Khartoum ta daina aiki tun lokacin da aka fara yakin basasa, don haka da alama ba za a iya daidaitawa ba.

Education Cannot Wait, ECW, ita ce asusun Majalisar Dinkin Duniya don ilimi a lokutan rikici.

Daraktar kungiyar, Yasmine Sherif, ta kai ziyara kasar Chadi a watan Mayu, inda ta yi alkawarin bai wa kasar Chadi dala miliyan uku domin samar da ilimi.

Tasirin yakin Sudan kan yara bai takaita ga ilimi ba kadai.

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar a ranar 12 ga watan Mayu cewa, wata masana’anta ta Sudan da ke samar da kashi 60 cikin 100 na abinci na musamman da ake amfani da su wajen magance matsalar karancin abinci mai gina jiki a kasar an lalata su saboda fadan.

Dubun dubatar yara a Sudan ne za su samu kansu cikin irin wannan hali.

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

LEADERSHIP Da CMG Sun Karfafa Dangantakar Aiki A Tsakaninsu

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.